Wednesday 26 October 2016

Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahadar Husaini (R.A) (3)

Dr. . Muhd Sani Rijiyar Lemo
Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahadar Husaini (R.A) (3)

Assalamu Alaikum,
A baya mun ji yadda Marubucinmu da abokan
tafiyarsa suka auka cikin wani kango wanda
waɗansu gungun mutane suke zaune cikinsa, ana
rera musu waƙe suna amshi. To mai ya faru
bayan shigarsu. As-Sheikh Ali at-Tantawi ya ci
gaba da cewa,
“Muka tsallaka sahu-sahu muka shiga. Jama’a na
zazzaune, duk sun yi shiru, kamar mutuwa ta
gitta, bayan da shi mawaƙin ya yi shiru, da alama
dai hutawa suke yi kafin su ci gaba.
Mun kutsa ciki ne har sai da muka isa sahun
farko inda mai bayar da waƙe yake bayarwa.
Yana zaune a kan kujera, a gefe da shi akwai
wasu ƙarin kujeru waɗanda babu kowa a kansu,
sai aka ba mu muka zauna. Ba da jimawa ba aka
ci gaba da rera waƙe. Duk sa’adda mawaƙin ya
rera wasu baitoci sai ya ɗan dakata kaɗan, can
sai ka ga su kuma sauran jama’ar sun ɗaga
hannuwansu sama sun tattake sun bugi ƙirajesu
da su, ji kake wani jib!! kamar katangar wannan
kango tana motsawa saboda ƙarar wannan bugun
ƙirji da suka yi. Sannan ya sake rera wasu
baitocin, su kuma su sake jibga hannuwansu a
kan ƙirajensu, har sai da ƙirajensu suka yi ja jawur
saboda tsananin duka, gumi ya jiƙa su sharkaf.
Kowa a cikinsu yana cike da baƙin-ciki da jimami
na abin da aka yi wa Husaini (R.A), zuciyarsa
kuma ta cika da gaba da ƙiyayya ga Banu
Umayya da mutanen Sham, waɗanda wannan
waƙen ya ɗorawa alhakin jinin Husaini (R.A).
Ana tsakar haka ne, sai kawai ɗaya daga cikin
ɗaliban da muke tare da su, allurar kirkinsa ta
motsa, sai ya mike tsaye wai zai gabatar da ni a
wajen wannan mawaƙi don ya nuna masa irin
ƙaunarsa gare ni, tare da fada masa girman
matsayina da martaba ta a gurinsu. Sai jin shi na
yi yana faɗawa maƙin nan cewa, ‘Wannan babban
malaminmu ne, kuma mutumin ƙasar Sham ne,
sannan kuma babban marubuci ne, ya yi wallafe-
wallafe dadama, a cikin littattafansa da akwai
littafinsa ma mai suna ‘Abubakar As-Siddiq’, da
kuma wani mai suna ‘Umar bn Alkhattab’, da …
da…” ya ci gaba da lissafa su. Ina!! Ai ban gama
jin ƙarshen maganarsa ba, sai kawai na shiga yin
kalmar shahada, don ta zama mini ita ce ƙarshen
maganata a zamana na duniya.
Ban sake fahimtar abin da wannan ɗalibi nawa
yake faɗa wa wannan mawaƙi ba, domin zuciyata
tini ta ɓallo ta faɗo ƙasan cikina, kamar yadda
kasan irin yadda ‘lifter’ take faɗowa daga dogon
bene yayin da sarƙoƙin dake ɗauke da ita suka
tsinke. Kawai ni a lokcin na saddaƙar mutuwa zan
yi. Na juya ina ta dube-dube ko zan ga maguda,
amma ina! Wuri ya cika maƙil, ga katanga ta
kewaye ko ina, babu mafita sai wannan ƙofar
ɗaya da muka shigo daga gare ta, tsakanina ko
da ita ban da waɗannan mutane masu kirji a
waje ba abin da nake gani. Sannan me kake
zaton zai faru idan mutanen nan suka gane
cewa, ni mutumin Sham ne?! Kuma ni ne
mawallafin littfin tarihin Abubakar da Umar?! Ta
yaya zan yi in tabbatar musu cewa, babu
hannuna a cikin kashe Husaini?! Kuma babu
hannun kakanni na a ciki, saboda su ‘yan asalin
ƙasar Masar ne, ba mutanen Sham ba ne?! Don
haka su fahimci babu hannuwansu a kashe
Husaini. Wai ma tukunna ma za su ba ni damar
in kare kaina ne har da zan musu wannan
bayanin? Kuma ma idan na yi ƙokarin kare kaina,
kuna ga ma za su yarda da ni ne har su gaskata
ni?!
Daga nan kawai na sakankance na gama yawo,
yau sai buzuna, abin da ya rage mini shi ne in ci
gaba da yin addu’a a asirce, idan na zo mutuwa
in yi mutuwa mai sauƙi, amma babu maganar
kubuta.
Shi kuma abokina Anwar fa, mai yake ciki, domin
shi ne ya shigar da mu wannan matsalar. Da na
saci kallosa sai na ga kamanninsa sun canza,
launinsa ya canza kala, ya koma ruwan kalar
lemon tsami. Na kalli fuskar Sayyid mai koren
rawani ko zan fahimci matakin da yake shirin
ɗauka a kain, sai ban fahimci komai daga
wajensa ba, na dai bar al’amarina a wajen Allah.
Muka ɗauki tsawon awanni saba’in a jere cikin
wannan hali na fargaba da firgici da tsoro, babu
wani abu da ya canza. Duk wani minti ɗaya
matsayin awa ɗaya nake ganinsa. Aka ci gaba da
waƙe har aka kai ƙarshe. Can sai na kula mutane
su fara shirin fita, don na ga suna ta ɗauko
rigunansu suna mayarwa jikinsu. To daga nan ne
na fahimci matsalata dai ta zo ƙarshe, hankalina
ya fara dawo wa jikina. Na dubi agogona sai na
ga ashe ba awanni saba’in muka yi ba, mintina
ashirin ne kachal. Tsabar dai tsananin firgicewa
ne kawai ya sanya na ga tsawon lokacin. Daga
nan na yi bankwana da ‘Sayyid’ na nufi ƙofa na
fita. Na ji ni kamar na mutu na dawo Duniya.
Muka kwana biyu a Hillah. Da muka sake haɗuwa
da ‘Sayyid’ muka tattauna, sai na fahimci shi ba
mai tsattsauran ra’ayi ne ba, (ko kuma dai taƙiyya
ya yi min). Sai nake tuna masa abin da ya faru,
sai ya ce, “Ka godewa Allah da ya kuɓutar da
kai, kuma bai bar wannan jama’a sun ji abin da
wannan ɗalibi naka ya fada ba”. Sai na ce, “Ashe
kai ba za ka kare ni ba idan sun so auka min?
Sai ya yi dariya ya ce, “Idan na kare ka, ni kuma
wanene zai kare ni?! Wallahi ba wata kariya da
zan ba ka, zan ƙale ka da su, ka fuskanci
makomarka!’…”.
Wannan shi ne yadda babban marubucinmu
Sheikh Ali At-Tantawi ya tsallake rijiya da baya,
yayin da ya tsinci kansa a tsakiyar ƙatti madaka-
ƙiraza, a Husainiyya ta garin Hilla cikin Ƙasar Iraƙi.
Ya rubuta wannan labari na shi a cikin littafinsa
mai suna ‘Az-Zikrayāt’, juzu’i na 3, shafi na
379-388. Allah ka ganar da su gaskiya. Amin

No comments:

Post a Comment