Monday 24 October 2016

NA GA 'MUTUWA' A RANAR TUNAWA DA SHAHADAR HUSAINI (R.A)​ Fitowa ta 1

NA GA 'MUTUWA' A RANAR TUNAWA DA SHAHADAR HUSAINI (R.A)
                                
                                                            Fitowa ta 1
✍ Rubutawa:            Dr Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo, Kano



As-Sheikh Ali at-Tantawi kawarren marubuci ne a cikin harshen larabci. Malami ne kuma tsohon Alkali ne, sannan kuma masanin larabci ne. Ya yi rubuce-rubuce masu yawa a fannonin ilimi daban-daban, kamar Tarihi, da Tarbiyya, da Siyasa, da Adabin Larabawa, da zamantakewa da al’adu.
    Ni dai ina matukar sha’awar karanta rubuce-rubucensa, kuma ina jin dadinsu, saboda kasancewa Sheikh Ali wani marubuci ne mai salon rubutu na musamman. Salon maganarsa yana da matukar dadin karantawa, ga shi ya kware sosai wajen sarrafa harshen larabci. Ni dai ban taba ganin marubuci mai iya ba da kwatancen abubuwa ba kamar Sheikh at-Tantawi, gaskiya ya kware a wannan janibin, idan yana maka kwatance kamar me! Sannan baya ga haka at-Tantawi mutum ne mai barkwanci, idan ya yi wata maganar sai ka ga mai karatu shi kadai yana ta dariya ba tare da na kusa da shi ya san dalilin dariyarsa ba. Don haka yake nishadantar da mai karanta littafinsa, idan ya fara karanta littafinsa ba zai so ya bari ba.
    Ina cikin karanta littafinsa ne mai suna “Az-Zikraayat” wato kamar dai ka ce a Hausa ‘Tina Baya’ ko kuma ‘Diary’ da Turanci. Ina tsakiyar karatunsa ne sai kawai na ci karo da wani tubutunsa mai dauke da waccen matashiyar ta sama. Na so a ce duk masu karanta wannan rubutu nawa za su iya karanta wancan rubutu na Sheikh at-Tantawi daga littafin da na ambata a cikin madarar larabcinsa. Saboda a gaskiya ta Allah ba na zaton akwai wani harshe wanda ba na larabci ba da za a fassara wannan makala tashi da shi kuma ya yi daidai da yadda take da larabcinta, a wajen fasaharta da gwanintar sarrafa harshe dake tattare da shi, tare da abin da ta kunsa na fadakarwa da ilimantawa mai yawa.
    Amma duk da haka zan iya tsakuro wa masu karatu dan taba-ka-lashe daga wannan makala ta Malam at-Tantawi. Amma fa ku fahimta fasahata da fasahar yaren da zan yi fassarar da shi, ko kusa ba za a daidaita shi da fasahar Marubucinmu ba da ta yaren Laraci harshen Al-Kura’ni, kuma harshen Annabin tsira, Allah ya kara masa salati da sallama. Amma dai da babu gwamma babu dadi.
Ku saurare ni ina nan tafe da tsakure Insha Allah. Allah ya sa mu dace.


Daga: ​ZAUREN FIQHUS SUNNAH

No comments:

Post a Comment