Sunday 12 March 2017

Sheik Daurawa ya nemi gwamnatin Katsina da ta kafa hukumar Hisba a


Daurawa Ya Nemi Gwamnatin Katsina Ta Kafa Hisba A Jihar

Daga Hussain Kabir Yar'adua

Babban malamin Addinin musulunci kuma kwamandan Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya nemi gwamnatin jihar Katsina ta kafa hukumar Hisba a jihar.

Malamin wanda ya gabatar da Wa'azi a Masallacin Juma'a na Bani Kumasi wanda Kungiyar Muslim Ummah suka shirya a a yau asabar yayi kira ga Gwamnatin ne lura da yanda ake ta kai korafe korafen saki, yawan barace barace DSS. Malamin ya bayyana kokarin da gwamnatin tayi a baya dasu ka  gabata inda ya zanta dasu ya kuma basu shawarwari don kafuwar hukumar a jahar. Malam ya bayyana irin alkairan da za'a samu karkashin hukumar.

Wa'azin ya samu halartar manyan mutane daga jihar kamar su Tsohon sufetan Yan sanda Alh Ibrahim Ahmadu Kumasie, shugaban Kungiya Muslim Ummah Na Jihar Katsina Dr. Misbahu Na'iya, Mai Shari'a Musa Danladi, Alh Muh'd Sanusi Wada, Mal Haris Isah Dukke, Mal Samu Adamu Bakori.