Thursday 15 November 2018

Matsalar yaduwar Fyade! a Katsina Laifin Wa?



Matsalar Yaxuwar Fyaxe! a Katsina  Laifin Wa?
Kwanakin baya wani babban jami’in 'yan Sanda ya zo ya same mu yake bayyana mana takaicinsu musamman ogansu kwamishinan Yan Sanda na Jihar Katsina C.P Muh'd Wakili, kan yadda yaxuwar fyaxen qananan yara ta zama ruwan dare a wannan jiha tamu. Jami’in ya labarta mana irin qoqari da jajircewar kwamishinan 'yan sandan kan yaqi da wannan mummunar xabi’a. Cikin jawabinsa wanda ya xau hankalina kuma nima na shaidi hakan shine, yadda mahukunta ke wancakalar da case na fyaxe musamman idan suna ganin za su mori wani abu daga wanda ake tuhuma. 
Ina jin ban tava baku labarin wani mai yin fyaxe da qananan yara ba wanda aka kama cikin azumi da rana qiri-qiri da yara guda biyu.  Shi wannan mai yin fyaxen ya shahara da aikata wannan kaba’ira, kuma ko an je ga hukuma sai ya sha, kwatsam da Allah ya yi nashi nufin sai ya haxu da wani jajirtaccen uba mai son bi ma xiyarsa haqqi, ya zo wajenmu yana kuka cewa don Allah mu taimaka mashi a qwato ma xiyarsa haqqinta, sai mu ka ce mashi za mu taimaka amman da sharaxin duk rintsi duk wahala ko a xan cinna mashi kuxi ba zai ja da baya ba, ya tabbatar mana da cewa wallahi ko mutuwa zai yi kan a hukunta mazinacin. A hakan ne Allah ya taimaka a kai ta faxi-tashi duk da tarin abokai da masu isa da shi mazinacin ke gare shi sai da aka kulle shi. Yanzu haka in bai sa wasa ba qila ya kusan haxa hardarshi, ga xan wanki da yake yi ana aje mai anini, yanzun shekarar shi ta uku saura shekara ashirin da biyu. Ba a fi sati ba wani case xin kuma wanda uban yarinyar ya salwantar da mutuncin yarinyar  shi ba.  Cikin wannan labarai za mu fahimci sakacin iyaye ma’ana da an xan basu kuxi 'yan qalilai sai su salwantar da mutunci xiyarsu.
 
Mahukunta ina nufin alqalai gaskiya suna taimakawa wajan yaxuwar wannan varna ta fuskar qin hukunta waxanda aka kama a irin wannan laifi, shi kanshi kwamishinan yan sanda na san wannan na daga cikin takaicinsa, don so da yawa jami’ansa za su gabatar da mai laifi amman qarshe da sun je kama mai rin wannan laifi sai su ga ai sun tava gabatar da shi, A vangaren jami’an tsaron ma kamar yadda vangaren iyaye, mahukunta to suma suna taimakawa wajan yaxuwar fyaxen ta yadda za su yi ta wahalar da miskinin uba ta hanyar zirga-zirga dss hakan sai yasa wasu iyayen su qosa qarshe su ga kuxin da su kashewa sun yi yawa don haka sun haqura. 

  • Kira na musamman ga Majalisar dokoki ta jihar Katsina shi ne akwai dokar da aka yi wadda ta ke Magana kan hukunta masu wannan xabi’a, muna qara tuni da Majalissar cewa ta dubi girman Allah ta zartas da wannan doka.

  • Kira na biyu ga Malamai magada Annabawa cewa, lallai Malamai suna da rawar da za su taka wajan magance wannan annoba musamman ta hanyar huxubobi, wa’azuzzuka dss.

  • Kira ga qungiyoyin lauyoyi musammaan na mata cewa su ma fa suna da babbar rawa wajan share ma waxanda aka zalunta ta hanyar fyaxe.

  • Kira na qarshe ga sauran al’umma shine su ne su ka fi kowa taka rawa wajan daqile wannan musiba ta hanyar kula da yara acikin ungawanni, makarantu dss.


Hassan Kabir Yar’adua
15/11/2018

Tuesday 22 May 2018

CACAR NAIJA BET A JIHAR KATSINA GWAMNATI YA KAMATA A TABBATAR DA DOKAR HARAMTATA



CACAR NAIJA BET A JIHAR KATSINA GWAMNATI
YA KAMATA A TABBATAR DA DOKAR HARAMTATA
Watanni kusan biyar da su ka gabata na so in yi rubutu kan wannan cacar, to amman kasancewar banda masaniya kan yadda ake yin cacar ya sa nai shiru, amman yanzun na samu bayani kan ta da kuma irin illarta ga al'umma.

Kamar yadda na nemi wani dan uwa yayi min bayaninta to ga amsar shi nan.

Mal Hassan ita naija bet wata caca ce da ta shafi wasanni musamman kwallon kafa da makamantanta. Wadda ada kake ganin wadanda ba musulmaiba a sabon layi suke da shaguna. Abinda akeyi shine zaka sa ka kudin akan dan wasa ko club kokuma coach bisa ga abinda zai faru ga wasan, kowanne akwati akwai adadin kudinsa sannan akwai farashin biya da zakayi idan kayi nasara kaci idan bakayi nasara ba shikenan. Idan kana kallon ball zakaga manyan turawa saman high table a stadiums ana yawan haskosu to sune jigajugan. Kuma ayqnzu anzamantar da abin sabanin da ta yadda zaka iya yi a internet kokuma zuwa shagonsu dake kusa da mutum yayanki kati kuma za'a shigar da mutum amatakin jiha ko kasa bakidaya. Akwai bet mai farashi tun daga N100 har zuwa wuce haka. Suna cewa ko nawa mutum yaci take zaiga kudinsa. Atakaice dai caca ce ta nejaful wadda muka sani abaya. Kuma ta shafi sanya kudi, wanda awani lokaci za'a baiwa mutum zabi na cewa akwai wasa tsakanin wane da wane ko club kaza da kaza. Sai akawo akwati kaza mai lamba kaza cewar club kaza zasu kaza wannan ma kaza zasu ci kaza. Kuma kowanne akwai kudinda mutum zai zuba. Kuma antsara hakan ganin kwallo ce tafi tasiri ga matasa. 

 

MAJALISSAR DOKOKIN JIHAR KATSINA 

Kwanan baya majalissa ta sanya doka kan wannan caca. Muna fatan zasu tabbatar da dokar haramta ta. Hassan Kabir Yaradua 22/05/2018

Wednesday 11 October 2017

GWAMNATIN JIHAR KATSINA NA SHIRIN BADA TALLAFIN KARATU A ISLAMIC ONLINE UNIVERSITY (IOU)
A wata zantawa da mai Girma Gwamnan Jihar katsina R.t Hon Alh Aminu Bello Masari yayi da Shugaban Jami’ar Shaharraran mai wa’azin addinai Dr. Bilal Phillips a lokacin da ya kai masa ziyarar Girmamawa a gidan Gwamnatin Jihar a ranar Alhamis 5 ga watan octoba, Shahararen Malamin ya gabatar da Jami’ar da yadda tsarin karatunta ya ke gudana. Wanda daga bisani Gwamnan jihar Katsina ya umurci mai bashi shawara kan harkar ilimin gaba da sakandire da ya tabbatar an bi hanyoyin da ya kamata don a samarwa al’umma guraben karatu a jami’ar. Dakta Bilal Philips ya zo garin Katsina ne don gudanar da Taron tunatarwa na kwana daya wanda Kungiyar Islamic Preaching and Public Services tare da hadin gwuwar HK Yaradua Islamic media su ka shirya taron mai taken ‘’Zaman lafiya da Bin Doka da Oda ga al’umma’’ taron wanda ya gudana ranar Juma’a 6/10/2017 a babban filin wasanni na Muhammad Dikko Stadium Katsina, an gudanar da taron cikin nasara wanda akalla sama da mahalarta 6000 ne su ka halarci taron wanda har da mabiya addinin kirista.
Daga cikin wuraren da Malamin ya ziyarta sun hada da Fadar mai-martaba sarkin Katsina Alhaji Abdulmumin Kabir Usman da kuma Jami’ar Al-Qalam University Katsina, Gidan Sheik Yakubu Musa Hassan Katsina (Sautus-Sunnah). Akwai kuma wasu Daliban Online University yan jihar Katsina, kungiyar Da’awah Family Support Katsina,haka nan kuma Kwamitin Masallacin Bilal Bin Rabah Katsina sun kawo ma Daktan Ziyara a masaukinsa.
Muna fatan wannan yunquri da gwamnatin jihar Katsina za tayi ya tabbata. Don wannan ba karamar dama bace ga al'ummar wannan jiha, muna kuma fatan gwamnatin za ta yi tsari na musamman don ganin an amfana da wannan jami'ar ta yanar gizo.
Usman Gambo Filin Samji
11/10/2017


Saturday 12 August 2017

A MAIDO DA SHARI'AR MUSULUNCI A JIHAR KATSINA

An yi kira da a maido da sharia'ar musulunci kamar yadda aka kafa ta a shekarun da su ka gabata. Malam Haruna Sani Na'ibin limamin Juma'a na Massalacin Jabir Bin Abdullahi da ke unguwar Kwado ya bayyana haka a wani wa'azi da aka gabatar a daren yau. Malamin ya bayyana haka ne da kuma yin kira da a kafa hukumar hisba. Daga nan Malamin ya ja hankalin jagoriri da su ji tsoron Allah su inganta aikin hajjin bana wanda shine aikin hajjin da alhazai su ka fi biyan kudi amman kuma su ka fi wulakanta.
Wadanan da wasu kiraye-kirayen sune abubuwan da Malamai guda 11 su ka dukufa suna yi don fadakar da wannan gwamnati.

Thursday 10 August 2017

RAN GADIN MU ZUWA ASIBITOCIN QANANAN HUKUMOMI



RAN GADIN MU ZUWA ASIBITOCIN QANANAN HUKUMOMI

Bayan rubutun da abokina Mubarak Rabi’u (Da’awah) yayi kan abokinsa da ya je General Hospital Katsina amman bai samu kulawa ba qarshe sai dai ya tafi wata Private asibiti akayi mashi magani. Wannan ne ya sa mu ka shirya tsaf domin fara ran gadin wasu daga cikin asibitocin gwamnatin jihar nan domin gano irin matsalolin da al’umma su ke fuskanta a cikin su fatan ko za a gyara.
Cikin ikon Allah jiya mun fara  ziyartar Comprehensive Health Care Batagarawa L.G wanda shine babban asibitin da ke cikin garin Batagarawa, Batagarawa L.G gari ne wanda babu gari mai fadin qasa a duk fadin jihar Katsina kamar sa amman abun da mu ka gani kuma mu ka ji ya tayar mana da hankali matuqa.
ABUN DA MU  KA JI KUMA MU KA GANI
Mun isa asibitin wajan 10:00pm isar mu ke da wuya mu ka shiga Male Ward anan mu ka tarar da yara Yan Makaranta guda 3 ba su lafiya, yaran su kadai ne sai wani yaro Prefect anan ne mu ka tambayi lafiyars u inda  suka bayyana mana cewa kwanan su uku anan amman  ba wata kulawa da ake masu, ba wani magani da aka rubuta masu ko aka basu, sai dai allurori da aka rubuta masu, a cikin dakin na Male ward babu tsafta ko kadan don kai kace wata ‘yar bola bola ce a ciki, sannan kofofin dakin gaba daya a 6alle su ke, ga sauro ga sanyi don gaskiya duk mai lafiyar da ya je ya kwana a dakin to lallai shima ana iya bashi gado to ina ga marar lafiya. Yaran wallahi sun zama abun tausai matuqa.
Bayan mun fito sai muka nufi Female ward anan ma mun ga yadda marasa lafiya su ke fama da kiran wani ma’aikacin jinya daga nan a kira shi ace jinin ya qare sai ka ji  acan ana qwala masa kira ana ga allurarr an kawo.
Bayan mun fito mun samu zantawa da wani mutum a cikin asibitin inda mu ka tambaye shi ya mu ka ga ma’aikacin can na jinya sai kiran shi ake  baya nan baya can, sai mutumin ya bayyana mana cewa ai shi kadai ne ke wannan aikin kullum haka yake fama a duk fadin asibitin ma’aikacin jinyar shi kadai ne. hakika a yadda mu ka ga ma’aikacin jinyar ya sadaukar da kansa ga wannan aiki sai na ga ai shi kanshi abun tausai ne. Mun je mun same shi mu ka gaisa mu ka tambaye shi ko shi kadai ne ma’aikacin jinya a cikin daren nan inda ya bayyana mana cewa ai duk fadin asibitin ma shi kadai ne kodayaushe yana cikin asibitin. Ya qara da ce mana aikin ya mashi yawa matuqa kawai dai yana yi ne don Allah, haka kuma ya bayyana mana  cewa marasa lafiya daga kusan local govt uku duk anan asibitin ake turo su. Rimi Local G da Charanchi  na cikin su inda har y ace mana yanzun haka akwai file na wani mara lafiya da aka turo mashi daga Rimi Local govt, sannan yace mana cikin dakin matan can akwai mara lafiyar da aka turo daga Jibia Local govt. ya bayyana mana cewa ai qwamma ma nan asibitin duk da ana ganin ta Comprehensive ce duk da ta Rimi General ce amman suna turo masu marasa lafiya wanda hakan ke gwada can Rimi sun fi fuskantar wannan matsalar. Wannan yasa a Ran gadin mu na gaba zamu tsallake Rimi da Charanchi muna fatan za a qara samun bayani daga wajan mazauna garuruwan.
SHAWARAR MU GA GWAMNATI
1. Muna mai bada shawara musamman ga mai girma gwamna wanda kulawar lafiyar al’ummar jihar Katsina duka tana wuyansa (ba Ciyamomi da mun ambace su) cewa ayi kokari a inganta asibitocin nan don gaskiya suna bukatar gyara fiye da gyaran da akayi ma makarantun  boko, sannan suna bukatar ma’ikata don da yawa daga cikin asibitocin nan ba ma’aikatan lafiya balle aje ga masu maintenance dss. Kuma gyaran wadanan asibitocin yafi a ciyo bashi a gina wasu asibitocin don wadanada za a gina din suma qarshe in ba a dau matakin gyaran tsaffin ba to kango za su koma.
2. Muna da dalibai masu yawa wadanda sun yo karatun nan amman suna nan suna zaman banza da gara-rambar yawo da CV. Inda za a dauke su lallai da an rage abubuwa da yawa.
Wannan shawarwarin ba wanda yafi cancanta a bas u kamar mai girma gwamna ko ince gwmantin jiha don wani na iya tunanin cewa mi ya shafi gwamnatin jiha da asibitin Local govt to wannan sai ya koma ya qara bincike lallai zai gano cewar gwamnatin jiha a mataki na farko ita ke da wannan alhaki. Sai kuma ga shi duka qanann hukumomin aljihun suna qalqashin gwamna to kun ga ko anan ma dole ne ita za a daura ma alhaki.
Daga qarshe wannan Rangadi mun yi shi ne ba don komai ba sai don fatan za a bincika a kuma dau mataki har ga Allah ba mu yi shi ba da nufin bayyana gazawar gwamnati ko su ka gare ta ba.
Mu kasance a ran gadi nag aba Insha Allah
Hassan Kabir Yaradua

08/10/2017





Friday 28 July 2017

ILLAR RABA MANYAN WAYOYI GA DALIBAN MAKARANTAR GWAMNATI TA FAMILY SUPPORT KATSINA.

ILLAR RABA MANYAN WAYOYI GA DALIBAN MAKARANTAR GWAMNATI TA FAMILY SUPPORT KATSINA.
Cikin azumin da ya gabata aka baiwa daliban wannan Makaranta manyan wayoyi kirar android tun daga yan aji 3 har zuwa 5.
Watannin da suka gabata mun taba rubutu kan irin yanda tarbiyar yaran makaranta ke tabarbarewa, ana cikin haka kuma sai ga batun raba wayoyi wanda munsan illar da ke tattare da waya a wannan zamani. Kwanakin baya munji wa'azi da ke bayanin fitintunun da ke tattare da wayoyin zamani. 
Mun samu rahotani tun daga cikin azumi zuwa yau irin yanda yaran suka tabarbare tun daga rashin maida hankali da kuma yawan sa chargi a masallatai da suke yi don su yi game da charting. Ni ganau ne a wani masallaci da nake zuwa Tafsir.
A binciken da muka gabatar a cikin wayar mun samu tabbbaci waya ce normal waya kamar sauran android kawai dai ansa wani Application na e-library wanda shima wai a wata-wata ake ma wayar subscription.
Mahaifan yara da dama sun nuna damuwarsu a satin da aka zauna mitin na iyayen yara a satin da ya gabata. Daya daga cikinsu ya bayyana "lallai su basu ji dadi ba da suka bar yaran suka amshi wayoyin ba saboda ni naga dana tsakar dare yana kallon badala da wayar, kuma koda yaushe yana online."
Da wannan makudan kudin da aka kashe wajen sanyan wayoyin nan da yara aka biyawa Waec da Neco da ya fi.
Allah ya datar da shuwagabaninmu  da yin ayyukan alkairi.
Muna kira ga gwamnatin jihar Katsina su ji tsoron Allah su amshe wayoyin.
Wannan photunan na kasa a wayar wani Ustazun yaro suke dan jss3 akwai masu munin da ban dauko su ba.



Monday 26 June 2017

GWAMNA YA SA A RUFE GIDAN GIYA


Alhamdulillah Yanzun ne ake min waya cewa Gwamna ya sa a rufe gidan giyar nan da muka ambata a jiya.
Allah ya sa kama gwamna da alkhairi ya sa a mizanin kyawawan ayyykansa.
Sannan kuma muna San qara shaidama mai girma Gwamna cewa akwai wasu gidajen duk da a lunguna suke wanda sums ya kamata a rufe. Daman ita barna wadda take bayyane ake magancewa.