Saturday 12 August 2017

A MAIDO DA SHARI'AR MUSULUNCI A JIHAR KATSINA

An yi kira da a maido da sharia'ar musulunci kamar yadda aka kafa ta a shekarun da su ka gabata. Malam Haruna Sani Na'ibin limamin Juma'a na Massalacin Jabir Bin Abdullahi da ke unguwar Kwado ya bayyana haka a wani wa'azi da aka gabatar a daren yau. Malamin ya bayyana haka ne da kuma yin kira da a kafa hukumar hisba. Daga nan Malamin ya ja hankalin jagoriri da su ji tsoron Allah su inganta aikin hajjin bana wanda shine aikin hajjin da alhazai su ka fi biyan kudi amman kuma su ka fi wulakanta.
Wadanan da wasu kiraye-kirayen sune abubuwan da Malamai guda 11 su ka dukufa suna yi don fadakar da wannan gwamnati.

No comments:

Post a Comment