KUSKUREN MALAM
KASET NE WANDA SHUGABAN YAN SHI'AR KATSINA MAL YAKUBU YAHYA YAYI BAYAN DAWOWARSA DAGA IRAN INDA YA BAYYANA HAKIKANIN ABUBUWAN DA YA GANO WANDA DA HAR YA TUBA AMMAN TALLALABIYA TA JA SHI YA KOMARUBUTAWA: Hasan Kabir Yar'adua
*NURUN ALA NUR "BAN SAKI AHLULBAITI BA NA KAMA SAHABBAI"*
*Fitowa Ta [01]*
Daga: *_Dr Mansur Ibrahim Sokoto_*
Labarin Sheikh Ali Dan Muhammad Al-Kadhibi - Wani malami dan kasar Bahrain da Allah ya ganar da shi gaskiya ya dawo daga rakiyar Shi'a.
GABATARWA;
“Godiya ta tabbata ga Allah, godiya mai yawa, mai tsarki, mai albarka wadda ta cike sammai da qasa da duk abin da Allah ya so bayan su. Tsira da amincin Allah su tabbata ga zababben bawansa, cikamakin manzanninsa; annabi Muhammad da iyalansa da sahabbansa da duk wadanda suka bi su da kyautatawa har rana ta qarshe. Bayan haka:
Na yi wannan dan rubutu ne don in zayyana ma mai karatu wasu ‘yan nazarce-nazarce da wasu ‘yan tambayoyi da na yi ma kaina har suka ja ni zuwa ga gaskiya wacce ban taba tunanin - a can baya – zan iya janyuwa zuwa gare ta ba.
Rikici ne ba na wasa ba, kuma aiki ne ja; mutum ya bar abinda ya saba da shi kuma ya gaje shi daga iyaye da kakanni idan ya gane cewa gaskiya ita ce sabaninsa. Ba ni kadai abin ya shafa ba, da yawa wadanda suka qarar da rayuwarsu a wajen kare wata manufa ko tabbatar da wata aqida, kwatsam! Sai Allah ya ganar da su cewa ba a kan daidai suke ba. A nan ne mutum zai yi ta fama da rikici a tsakanin sa da zuciyarsa amma idan ya daure sai Allah ya yi ma sa gamon katar. A nan ne mutum zai gane cewa, riqo da rubabbiyar aqida don kawai son zama tare da ‘yan uwa da dangi bai kamata ba. Idan mutum ya yi haka to, ya yi cinikin duna wanda ba shi da riba sai hasara. A maimakon haka kamata ya yi mutum ya yi riqo da gaskiya a lokacin da ta bayyana gare shi."
Baban Khalifi
Muhammad Al-Qadhibi
TUNA BAYA;
Tun da farko na tashi a gidanmu na tarar da iyayena masu tsananin kula da riqo da addinin Shi’a. Ban yi wayon sanin mahaifina ba sai dai kawuna wanda ya riqe ni tsakani da Allah bayan mutuwar mahaifin nawa. Kawuna yana cikin shehunai masu rawani, kuma ya yi karatu a Hauza ta yankin Jadd Hafs a qasar Bahrain, bayan nan kuma ya samu qarin ilimi a babban birnin Qum na qasar Iran.
Ba zan manta yadda kawuna yake kula da mu yana ba mu tarbiyya ba, yana hana mu cudanya da bata gari don kada su gurnata mu. A ranar da ya ji ina cewa zan karanci ilimin kida a jami’a idan na gama makarantar sakandare bata ransa ya yi, sannan ya kira ni cikin lumana ya lurar da ni, ya ce, ka ga ni, sa’ad da nake yaro irinka ban samu mai dora ni a kan hanya ba. Ya rinqa rarrashi na har ya canja min ra’ayi. Wataqila da yanzu ni wani shahararren makadi ne.
Mahaifiyata ita kuma ba ta da aiki sai jiran lokutan bukukuwa wadanda ake yi akai-akai don raya addinin Shi’a. Tana bugun gaba da shiga a cikin su tana ganin – ta haka – za ta samu falalar hidimar sayyidi Husaini. Sau da yawa takan je bukukuwan ko ba ta da lafiya. In aka yi ma ta magana sai ta ce, ai shiga wannan sha’ani shi ne maganin ciwonta. Mahaifinta kuwa sana’arsa ita ce yin ganguma da ake kida da su a bukukuwan Ashura da sauran bukukuwa da makokai da ake yi a koda yaushe. Wani abin da mai karatu zai so ya sani shi ne cewa, dukkan mu muna bin tafarkin shehun malami ayatullahi.
Sabon saqon Boko Haram: tunatarwa ga jami'an tsaron Nigeria.
Tun ba a yi nisa ba, Marigayi Shaikh Ja'afar Mahmud Adam ya bayyanawa duniya, ya sirrintawa mahakunta hatsarin Da'awar Boko Haram, qarshe Allah Ya rubuta masa shahada a hannun miyagu yana sallar asuba daren juma'a, Allah Ya masa Rahama Ya kyautata makwanci.
A wani wa'azin Izala da aka yi a garin Maiduguri, ana tsakiyar Boko Haram, Shaikh Sani Yahya Jingir Allah Ya qara lafiya Ya kare shi, ya hau minbari ya bayyanawa duniya Boko Haram ba musulunci bane, kuma ya shawarci mahakunta su tsananta sa ido da tsaurara matakan daqile tunani da ta'addanci irin na Boko Haram. Sakamakon haka 'yan ta'adda suka kai masa hari da boma-bomai da bindigogi yana tafsirin al-Qur'ani, Allah Ya tserar da shi, amma an rasa rayuka, ciki har da dan Shaikh Muhammad Nasir AbdulMuhyi.
Shaikh Albani Allah Ya ji qansa shi cewa ma ya yi idan dan Boko Haram ya shigo masallacin sa, za su yi dauki-ba-dadi, sabo da yadda kowa ya fada musu a kan halaka su ke amma sun qi ji, a lokacin kuma suna nema su gagari jami'an tsaro, qarshe Allah Ya masa shahada a hannun 'yan ta'adda.
Malaman sunnah da suka rasa rayukansu a kan fada da Boko Haram ba za su lisaafu ba amma hakan bai hana su ci gaba da fafatawa ba. An ga yadda Shaikh Isa Ali Pantami da Mal Idris AbdulAziz suka yi muqabala a bainar jama'a suka bayyanawa 'yan Boko Haram kuskuren fahimtar su ga addini, tun ma Muhammad Yusuf na da rai, tun Boko Haram bata fada hannun 'yan sari irin yanzu ba.
To Malaman Sunnah ba su yi qasa a gwiwa ba, amma maganar ita ce, an san tushen aqidar Boko Haram jagoran 'yan shi'a ne, Zazzaki, wanda yanzu haka yake hannu, ya kawo ta Nigeria. An sani sarai, Zakzakiy ne ya fara cewa Boko Haram ne a wajajen 80s, ya sa mutane suka fice daga makarantu, wasu ma sun gama suka riqa yayyaga takardun su. Sannan an ruwaito shi kansa Muhammad Yusuf tsohon almajirinsa ne, daga bisani ya tuba, tuban muzuru. A bakin Zakzakiy kalmar 'bara'a' ta bayyana a tsakanin matasa, wanda har yanzu 'yan shi'a suna qudurce da ita, har da wani Chemist na gargajiya wai shi 'Bara'a Chemist'.
Ma'anar bara'a ita ce abin da Boko Haram suka yi, wato raba gari da duk wani tsarin gwamnatin Nigeria sabo da ba tsarin Allah bane, ba tare da la'akari da halin da aka sami kai a ciki na zamantakewa tsakanin Musulmi da wadanda ba Musulmi a qasa daya ba. Qarqashin wannan ne za a ji suna cewa 'ba hukuma sai ta Allah' ma'ana ba su yarda da gwamnatin Nigeria ba sai ta Zakzakiy da ta Iran kamar dai yadda Boko Haram ba su yarda da ita ba sai ta Shekau da ISIS.
Wannan ita ce Aqidar 'yan shi'a kuma ba sa musu a kan haka.
Duk wanda ya bibiyi maganganun Zakzakiy a kan Boko Haram, ya san aqidar Zakzakiy ita ce 'ba Boko Haram, gwamnati ce Boko Haram'. Mutane da yawa, la'alla har wasu cikin jami'an tsaro, basu fahimci me Zakzakiy yake nufi ba. Da yawa suna fahimtar yana nufin babu wasu mutane 'yan Boko Haram masu aqidar Boko Haram, amma ba haka bane. Zakzakiy ya san awai su, amma yana nufin su 'yan Boko Haram su ne suka fi kusa da gaskiya, ita gwamnati ita ce Boko Haram, 'yarta'adda.
Don haka Zakzakiy yana ganin za su iya haduwa da Boko Haram don a hambarar da gwamnatin Nigeria daga baya sa daidaita tsakanin su, amma ba za su iya haduwa da gwamanti su ga bayan Boko Haram ba in yaso sa sasanta tsakanin su daga bisani.
Kamar yadda zai wa gwamnati wahala ta samo kan Boko Haram cikin laluma sabo da alaqar da Boko Haram din ta qulla da ISIS, haka ma 'yan Shi'a, domin su kuma daga Iran ne kawai za a basu umarni su karba. Ita kuma Iran ba za ta bada wani umarnin gaske wanda ba na tada hankali da yi wa hukumomi bore da gwagwarmayar juyin-juya-hali ba. Za a iya ganin haka, a yayin da mahakuntan Saudi Arabia ke hado hancin qasashen musulmi don yaqar munanan aqidu irin na ISIS da Boko Haram da Hizbolla da sauransu, ita Iran baza mugga-muggan makamai take yi a qasashe, hatta nan Nigeria an kama jirgin ruwa maqare da makamai daga qasar Iran, da kuma wasu dandazon wasu makaman a Kano a hannun 'yan shi'a.
Alhamdu lillah, malaman sunnah sun yi aiki tuquru wajen tsare tunani da aqidar jama'a, kuma ba fargabar ko wace irin matsala, amma babbar matsar da dole za ta kasance in ba a yi wa tufkar hanci mai qarfin gaske tun qafin ta fara bajewa ba ita ce ta shi'a.
Insha Allah za mu ci gaba da bayyana hatsarin 'yan shi'a a qasa da yadda za su zo su fi Boko Haram barna idan ba a dauki qwararan matakai tun yanzu ba.
Allah Ya tsare mu da tsarewarsa Ya bamu zaman lafiya a qasarmu Nigeria.
CIKAKKEN BAYANI AKAN GHADIR KUM
Daga Bakin: Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemu
Dama haka abin yake, lallai Allah ya taimake ni da na saurari wannan tattaunawa ta Dr Muhammad Sani Umar R/Lemu, tabbas Dr ya tabbata bijimin Malami mai ilimi da kuma adalci. An kusa a ruftani amma Allah ya taimake ni gaskiya tayi halinta. Kai Alhamdulillah!!! A’ah kai Jama’a!!!
• Wai kasan mai ake kira da GHADIR KUM?
• Mai ya faru ne a wannan waje?
• Da gaske ne Annabi yayi Huduba ko kuma dai kawai shifcin gizo ne?
• Idan yayi Huduba to mai yace?
• Anya ba’ayi karin gishiri a Hudubar ba idan ma har ya tabbata yayi Hudubar?
• Kai jama’a!!! Karba fa nima na zama cikin Jahilai wanda ake wasa da hankalinsu!
• Bazan taba yadda wannan al’amari ya wuce ni ba, sai naji yaya abin yake!
Don jin cikakken abin da wannan bayani ya kunsa kai tsaye kayi downloading ta wannan link dake kasa. Ayi sauraro lafiya……………………….
↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓
http://www.dandalinsunnah.com/multimedia/amb/others/Lecture/DrSani/Ghadir%20Kum.mp3
↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑
Idan wannan bai yiba a wayar ka, za ka iya downloading ta wannan link din na kasa.
↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓↓
http://files.mboxdrive.com/1470856927/Ghadir%20Kum.mp3
↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑
saboda samun karin bayani adai kan shi wannan batu kar a rifta da kai, ga rubutattun makala da Shehin Malami Salihu Baban Takko ya rubuta ta waddannan links dake kasa
darasi na farko: https://m.facebook.com/photo.php?fbid=4848453588006&id=1796968402&set=a.1724436649535.69364.1796968402&refid=17
Darasi na biyu: https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=4852911379448&id=1796968402&refid=17
Allah ya kara nuna mana gaskiya gaskiya ce ya bamu ikon binta, ya nuna mana karya karya ce ya bamu ikon guje mata.
↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑↑
-GHADIR: KALUBALE GA ‘YAN SHI’A(Dr. Mansur Sokoto)
INGANTACCEN LABARIN GHADIR:
Kalmar Ghadir a larabce, tana nufin wurin da ya tara ruwa da ciyawa.
“Ghadir Khum” sunan wani tafki ne da yake a yankin Juhfa, kilomita 15 daga Rabigh. Nisan sa daga Makka kilomita 160 ne.
Labarin Ghadir:
Annabi Sallallahu Alaihi wa Sallam ya aiki Khalid dan Walid a matsayin kwamandan rundunar da za ta yi yaki a kasar Yaman daf da fara aikin Hajjin shekara ta 10H, hajjin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da kansa ya jagoranta.
Bayan da rundunar musulmi ta ci nasara sai Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya aika Sayyidi Ali don ya kula da sha’anin Ganimar da aka samu.
Ali Radhiyallahu Anhu ya raba Ganima, kuma ya cire hakkin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam na Khumusi kamar yadda Alkur’ani ya zayyana. Daga ciki kuma ya cire ma kansa wata kuyanga da ta ba shi shawa.
Sayyidi Ali bai bata lokaci ba ya zarce zuwa Makka don ya riski maigidansa Sallallahu Alaihi wa Sallam a wurin aikin Hajji. Ya kuma wakilta wani daga cikin sojoji akan sauran aikin da ya rage.
Domin ya dadada ran sojojin, wakilin Sayyidi Ali ya raba ma su tufafi kyawawa daga cikin abin da aka ganimanto. Ya kuma yi ma su izini kowa ya hau rakumin da yake so daga cikin kayan Ganima. Kafin haka, sojoji sun gabatar da bukatar haka ga Sayyidi Ali amma bai amince ba. Sai ya ce ma su, rabonku sai an je Madina.
Sojojin wannan runduna sun hadu da Sayyidi Ali tare da Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam a kan hanyar su ta dawowa bayan gama aikin Hajji. Sayyidi Ali ya nuna rashin jin dadinsa a kan wannan rabo da aka yi kafin lokacin yinsa. Nan take ya yi umurni duk su sauka daga rakuman, suka kuma mayar da tufafin da aka raba masu. Rayukansu sun baci matuka a kan haka kuma sun kai karar sa ga Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam suna zargin sa da cewa ya kuntata masu.
Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya iso Ghadir Khum, kuma ya lura da fushi a fuskar wadannan sojoji. Ya yi huduba yana tambayar su
(!ألستُ أولى بالمؤمنين من أنفسهم؟)
“Ashe ban fi muminai cancanta da kawunansu ba?” Suka ce masa, haka ne. Sai ya ce,
(فمن كنت مولاه، فعلي مولاه)
“To, duk wanda nake majibincinsa Ali ma majibincinsa ne”. Ma’ana, bai dace ku bata ranku a kan hukuncin da ya yi ba.
Da wannan babban jagora ya kwantar da wannan rikici da rashin fahimta, ya kuma nuna wajabcin a yi ma jagora da’a, sa’annan ya bayyana matsayin dan uwansa Sayyidi Ali a wurin muminai. Sojojin suka ba shi hakuri, suka gane matsayinsa, suka wuce Madina tare da sauran ayarin mahajjata da suke tare da shi.
Wannan shi ne abin da ya faru. Illa iyaka.
TATSUNIYAR GHADIR
‘Yan Shi’a sun ribaci wannan abin da ya faru kuma ya zo ya wuce kamar sauran ire-irensa. Suka fankama shi, suka fadada shi, suka mayar da shi wani gagarumin bukin nadin sarauta. Suka kuma jefi duk Sahabban Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da kin Allah da kauce ma gaskiya, da jayayya da wannan nadi da suka ce an yi.
Wannan akidar ta Ghadir a matsayin ranar buki ba a san ta a cikin tarihi ba sai bayan sama da shekaru 340 gwamnatin Shi’a ta Buwaihawa ta kago wannan bidi’a a kasar Iraqi. Suka mayar da ranar 18 ga watan Dhul Hajji a matsayin ranar wannan buki ta kowace shekara. Sukan taru a wurin kaburburan manyansu suna ta kururuwa suna la’antar masoyan Allah wadanda suka ce sun kauce ma umurni Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da ya bayar na mika mulki ga maigida Sayyidi Ali.
Sun kago ruwayoyi barkatai a kan falalar wannan rana, cikin su har da cewa wai, Imam Ar-Ridha ya ce, da mutane sun san matsayi da falalar wannan rana da Mala’iku sun rinka musafaha da su har sau goma a kowace rana.
Haka kuma sun kitsa tatsuniyoyi masu nuna wai, manyan Sahabbai sun yi ma Ali mubaya’a amma a munafurce, sannan suka shirya makarkashiyar kashe Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam. A cikin su kuma wai har da duk sauran tara daga cikin mutane goma da Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya yi ma su bushara da aljanna.
KALUBALE GA ‘YAN SHI’A
Muna kalubalantar ‘yan Shi’a a kan wannan batu da wadannan tambayoyi:
1. Idan wannan magana ta Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam cewa “Duk wanda nake majibincinsa Ali ma majibincinsa ne” tana nuna wajabcin shugabantar da shi, to me za ku ce game da fadar Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam “Ko wace al’umma tana da amintacce, mu kuma amintaccenmu a cikin wannan al’umma shi ne Abu Ubaida”? Wa ya fi cancanta a cikin su kenan?
2. Idan har gaskiya ne an yi wannan nadin kamar yadda kuke cewa, me ya sa ba a umurci Sayyidi Ali da ya ci gaba da ba da Sallah ba musamman bayan da ciwon ajali ya kama Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam?
3. Me ya sa ba ayi wannan bukin a zamanin da Sayyidi Ali yake Khalifa ba ko Sayyidi Al-Hasan ko a zamanin duk Imamanku goma sha daya da suka rayu kafin Malam Na-boye (Mahadinku) ya zo duniya? Me ya sa sai lokacin da Buwaihi Bafarise mai kamun kifi ya kafa gwamnati sannan aka fara wannan buki a shekarar 352H?
4. Idan hudubar Ghadir tana nufin nadin sarauta ne, me ya sa ba ayi ta a Makka ba in da duk alhazan duniya suka taru su sama da mahajjata dubu dari?
5. Ashe Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam bai yi hudubobi a can Makka da Minna da Arafat ba? Me ya sa bai ware huduba ta musamman a kan wannan babbar maganar ta halifancin Sayyidi Ali ba?
6. Ashe Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam bai yi huduba a kan jinainai da dukiyoyi a ranar babbar sallah ba? Ashe bai yi ma al’umma wasici da muhimman abubuwan da suke bukatar sani ba? Ita wannan maganar ba ta kai muhimmancinsu ba ne ya manta da ita? Me ya sa sai da aka watse, kowa ya bi hanyar garinsu saura mutanen Madina kawai suka rage sannan ya yi wannan magana a cikin sunkurmin daji a tafkin Ghadir?
7. Ya ya aka yi Sahabbai suka riwaito wannan hudubar ta Ghadir alhalin kun ce sun boye kaso biyu cikin uku na Alkur’ani masu bayyana falalar Ahlulbaiti?
8. Kun ce duk rikicin da musulmi suka shiga a tsawon tarihi dalilin kauce ma wannan umurni na ranar Ghadir ne da sahabbai suka yi. Me ya sa Alkur’ani ya yi biris da labarin Ghadir?
9. Allah Tabaraka wa Ta’ala ya saukar da sura ta musamman a cikin Alkur’ani kan maganar Hudaibiya da mubaya’ar da sahabbai suka yi ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da har wuri da bishiyar da suka yi mubaya’a a karkashinta, kuma ya ce ya yarda da su a kan haka bisa ga abin da ke cikin zukatansu na imani da ikhlasi. Kuma ya ce, a lokacin da suke yi ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam mubaya’a hannun Allah yana saman nasu. Me ya sa idan har an yi wannan mubaya’a Allah bai kawo ta ba a cikin Alkur’ani?
10. Mubaya’ar da mata suka yi ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ita ma Allah ya kawo labarinta cikin Suratul Mumtahana. Shin ita wannan mubaya’ar ta Ghadir ba ta da muhimmanci ne irin wannan mubaya’ar mata ko kuwa?
‘Yan Shi’a ku ji tsoron Allah! Malamanku suna zargin Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam da boye wannan bayani wai a cikin Makka har suna cewa a kan wannan boyewar da ya yi sai da Allah ya saukar da ayar ”Ya kai wannan manzo ka isar da sakon da aka saukar ma ka daga wurin Ubangijinka. Idan kuwa har ba ka yi ba to, ba ka isar da sakonsa ba. Kuma Allah zai kare ka daga mutane”. To, sannan wai, ya tsaya a Ghadir Khum ya isar da wannan sako. Ku ji tsoron Allah! Ku darajanta manzonsa, ku koma ga gaskiya.
Wallahi, Sayyidi Abubakar da Sayyidi Umar da Sayyidi Usmanu da ma duk sauran sahabbai almajiran Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ba su jiye ma Sayyidi Ali da kome. Kuma ba su da wani kwadayi ga duniya balle su nemi shugabanci. Allah Ta’ala da kansa cewa ya yi a kan su:
(للفقراء المهاجرين الذين أُخرجوا من ديارهم وأموالهم يبتغون فضلا من الله ورضوانا وينصرون الله ورسوله أولئك هم الصادقون)
“-A bayar da Fai’i- ga talakawa Muhajirai wadanda aka fitar da su daga gidajensu da dukiyoyinsu suna neman falala daga Allah da yarda, kuma suna taimakon Allah da manzonsa. Wadancan su ne masu gaskiya”
To, ka ji. An kore su daga garuruwansu, aka kwace dukiyarsu kuma a cikin zukatansu ba zaman gida ko mallakar dukiya ne a gabansu ba. Babban gurinsu shi ne taimakon Allah da manzonsa. Ka kuma ji Allah ya ce ma su masu gaskiya. Don Allah ta ina wadannan za su yi kwacen mulki kuma har su shirya ma Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam makarkashiyar kisan sa?!
Ya Allah! Ka shiryar da bayinka, ka ceto su daga muguwar akidar da Farisawa ‘yan bautar wuta suka kago suka lullube ta da rigar musulunci don su halaka su. Allahumma Ameen
LALACIN GABOBI DA LALACIN KWAKWALWA!
Wannar Muhimmiyyar Lacca ce wacce Sheikh Aliyu Said Gamawa (Sarkin Malaman Gamawa) Ya gabatar. Kuma tana kunshe da Nasihu Masu Tsada da Muhimmanci ga Al'umman Musulmi Musamman Matasa a wannan Zamani da muke ciki.
Kana iya sauraron Cikakkiyar Laccar ta wannan Link dake Kasa:
http://www.dandalinsunnah.com/multimedia/amb/muhadara/1437/LalacinGabobi_da_LalacinKwakwalwa_By_ShAliyu_Sa'id_Gamawa.mp3
.
.
.
MINBARIN SUNNAH
Facebook : @ http://www.fb.com/minbarinsunnah
WHATSAPP : @ +2347066677977
Abdulmuttalib Abdullahi
INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR
RAJI'UN:
ALLAH YAYIWA UMMUL FADHIL
YUSRA ABIDEEN RASUWA A
SAFIYAR YAU LAHADI, MATAR
BABBAN MALAMIN HADISI
MASANIN ALLAH DA SUNNAH
SHAIKH NASIRUD DEEN ALBANY
RASUWA,TANA YER SHEKARU
86.
ALLAH YASA ALJANNAH CE
MAKOMARTA.
Engr Basheer Adamu Aliyu
FOREWARNED IS FOREARMED!
Kidnap experience on Abuja Kaduna highway:
Forwarded as received. Experience of a Snr
Military Officer on Sep 1 along Abuja-kaduna
express way.
I wish to share a terrible experience I had on
Thursday 1 September 2016, along Kaduna-Abuja
highway at about 9pm. I had good intelligence on
the security situation and considered that it was
still ok to move based on that knowledge. I and a
family friend were travelling to Abuja and we had
left by 6pm. Our car had some problems and we
finished fixing it by 8pm. We then proceeded on
the trip. We had just passed Redeemed Camp, by
Alheri, where we saw 2 white coloured J5 buses.
The last mileage I saw was 138 KM to Zuba & I
saw the 2 buses along the road parked left and
right on the shoulders. I told my friend that this
looked like a kidnap spot, that it had all the
features like a bend and a slope with the buses.
My friend then screamed that they were throwing
knockouts at us immediately I finished saying
that. I quickly realized that it was gunfire from
AK-47. Three men stood in front of the road
firing at us. I slammed the brakes, the car
veered right and I decided to continue right, off
the road. I was able to stop the car before a
ditch I saw. I tried to reverse but it didn't
engage, the car engine went off and some
attempts to restart it failed. Then one of them
ran to me, I came out of the car with my hands
up, so also my friend. Then, I turned back and
started pacing. The guy that came for me looked
like a foreigner, from Niger. Then we bolted.
They started firing at us. Then someone came
from our initial behind and started shooting at
us. We managed to cross the road with nothing
in sight; No cars etc. We couldn't even see the
road divider. Then we both crossed the road.
They chased us and kept shooting. That was
how we escaped and pinned down in the bush.
Immediately we were on the other side of the
road we entered the bushes and kept running.
During this time, for over 2hrs they came with
their car patrolling in search for us. Later the
police came, there seemed to been some
collaboration amongst them. I lost my Fone and
other valuables, but my luggage in the booth was
intact as the booth didn't open since it was a
406. It happened like a movie but its real. They
weren't herdsmen,They were the kidnappers
along that axis. They exist in some areas up
north.
Don't travel when it's dark.
Always watch out well in bends, slopes and hills.
Be careful about any checkpoints, not all
checkpoints are real.
The police helped to stop all cars when the
operation started with us to enhance smooth
operation by the kidnappers.
The kidnappers were operating under the cover
of two police checkpoints in about a kilometre
apart.
The police tried to take us back to the scene
which I refused clearly and instead called on the
army.
That was what forced the police to take us to
the nearest army post.
Don't travel when it's dark as it increases the
risk, but note also that same technique would
work even in day time.
Lessons learnt:
If uve to run for ur life take the first chance and
don't be afraid of the gun when ur running.
Usually, guns are effective at close range.
Most people including uniformed men are poor
shooters especially when it has to do with
moving targets; this fact is unknown to many
including the uniformed men.
I've seen fire but not this sort of unexpected fire.
If ur car breaks down on the road and ur
stranded, do not remain inside it or near it. My
advise is for u to cross the road and look for a
nearby village. An abandoned car would always
attract anyone including criminals. If uve to flee
into the bush in a pursuit, run in a diagonal axis
to the road.
In a near death experience u don't bother about
the things u did, u worry more about the things u
didn't do.
The kidnappers were actively collaborating with
the police.
ﻟﻘﺪ ﺃﻣﺮﻧﺎ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰﻭﺟﻞ ﺑﺼﻠﺔ
ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﻭﺍﻟﺘﻮﺍﺻﻞ ﻣﻌﻬﻢ ﻭﺑﺮﻫﻢ
ﻭﺍﻹﺣﺴﺎﻥ ﺇﻟﻴﻬﻢ، ﻭﺣﺬﺭﻧﺎ ﻣﻦ
ﺍﻟﻘﻄﻴﻌﺔ ﻭﺧﻄﻮﺭﺗﻬﺎ ﺣﻴﺚ ﻻ
ﻳﺪﺧﻞ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﻗﺎﻃﻊ ﺭﺣﻢ، ﻭﺻﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﺗﻜﻮﻥ ﻣﻦ
ﺧﻼﻝ ﺯﻳﺎﺭﺗﻬﻢ ﻭﺍﻻﻃﻤﺌﻨﺎﻥ ﻋﻠﻴﻬﻢ ﻭﺍﻟﺴﺆﺍﻝ ﻋﻨﻬﻢ ﻋﻨﺪ
ﻣﺮﺿﻬﻢ ﻭﺍﻟﺪﻋﺎﺀ ﻟﻬﻢ ﻋﻨﺪ ﻣﺼﺎﺋﺒﻬﻢ ﻭﻣﺴﺎﻋﺪﺗﻬﻢ ﻓﻲ
ﻛﺮﺑﺎﺗﻬﻢ ﻭﻋﺜﺮﺍﺗﻬﻢ، ﻭﻣﺸﺎﺭﻛﺘﻬﻢ ﺃﻓﺮﺍﺣﻬﻢ ﻭﺃﺣﺰﺍﻧﻬﻢ
ﻭﺍﺳﺘﻀﺎﻓﺘﻬﻢ ﻭﺇﻛﺮﺍﻣﻬﻢ .
ﻣﺎ ﺍﻟﻤﻘﺼﻮﺩ ﺑﺎﻷﺭﺣﺎﻡ؟
ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﻫﻢ ﻛﻞ ﻣﻦ ﺗﺮﺑﻄﻨﺎ ﺑﻬﻢ ﺻﻠﺔ ﻧﺴﺒﻴﺔ ﻣﻦ ﺟﻬﺔ
ﺍﻷﻡ ﺃﻭ ﺍﻷﺏ، ﻭﻳﺪﺧﻞ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻦ ﺗﺮﺑﻄﻨﺎ ﺑﻪ ﺻﻠﺔ
ﺳﺒﺒﻴﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﻨﻜﺎﺡ ﺃﻳﻀﺎً ﻭﻫﻢ ﺍﻷﺻﻬﺎﺭ .
ﺇﺫﺍ ﺃﺭﺩﺕ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻭﺍﻟﺴﻌﺎﺩﺓ ﻓﻌﻠﻴﻚِ ﺑﺼﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ، ﺇﺫﺍ
ﺃﺭﺩﺕ ﻃﻮﻝ ﺍﻟﻌﻤﺮ ﻓﻌﻠﻴﻚِ ﺑﺼﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ، ﺇﺫﺍ ﺃﺭﺩﺕ
ﺍﻟﺮﺯﻕ ﺍﻟﻜﺜﻴﺮ ﻭﺍﻟﻮﻓﻴﺮ ﻓﻌﻠﻴﻚِ ﺑﺼﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ، ﻓﺴﺒﺤﺎﻥ
ﺍﻟﺨﺎﻟﻖ ﺍﻟﺬﻱ ﺟﻌﻞ ﻟﻨﺎ ﻣﻦ ﻋﺒﺎﺩﺓ ﻳﺴﻴﺮﺓ ﻓﻀﻞ ﻭﺛﻮﺍﺏ
ﻭﺟﺰﺍﺀ ﻋﻈﻴﻢ .
ﻣﺎ ﻫﻮ ﻓﻀﻞ ﺻﻠﺔ ﺍﻟﺮﺣﻢ؟
• ﺻﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﻫﻲ ﻃﺎﻋﺔ ﻟﻠﻪ ﻋﺰﻭﺟﻞ : ﻟﻘﺪ ﺃﻣﺮﻧﺎ ﺟﻼ
ﻭﻋﻼ ﺑﺼﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ } ﻭَﺍﻟَّﺬِﻳﻦَ ﻳَﺼِﻠُﻮﻥَ ﻣَﺎ ﺃَﻣَﺮَ ﺍﻟﻠّﻪُ ﺑِﻪِ
ﺃَﻥ ﻳُﻮﺻَﻞَ ﻭَﻳَﺨْﺸَﻮْﻥَ ﺭَﺑَّﻬُﻢْ ﻭَﻳَﺨَﺎﻓُﻮﻥَ ﺳُﻮﺀَ ﺍﻟﺤِﺴَﺎﺏِ {
ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺮﻋﺪ .21
•ﺻﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﺗﺠﻠﺐ ﺍﻟﺮﺯﻕ ﺍﻟﻮﻓﻴﺮ : ﻗﺎﻝ - ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ
ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ :- (ﻣﻦ ﺃﺣﺐ ﺃﻥ ﻳﺒﺴﻂ ﻟﻪ ﻓﻲ ﺭﺯﻗﻪ
ﻭﻳﻨﺴﺄ ﻟﻪ ﻓﻲ ﺃﺛﺮﻩ ﻓﻠﻴﺼﻞ ﺭﺣﻤﻪ ) ﺭﻭﺍﻩ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ِ،
ﻭﻋﻨﺪ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﺃﻥ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ - ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ
-ﻗﺎﻝ : ( ﺗﻌﻠﻤﻮﺍ ﻣﻦ ﺃﻧﺴﺎﺑﻜﻢ ﻣﺎ ﺗﺼﻠﻮﻥ ﺑﻪ ﺃﺭﺣﺎﻣﻜﻢ،
ﻓﺈﻥ ﺻﻠﺔ ﺍﻟﺮﺣﻢ ﻣﺤﺒﺔ ﻓﻲ ﺍﻷﻫﻞ، ﻣﺜﺮﺍﺓ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺎﻝ،
ﻣﻨﺴﺄﺓ ﻓﻲ ﺍﻷﺛﺮ ) .
• ﺻﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﺳﺒﺐ ﻟﺪﺧﻮﻝ ﺍﻟﺠﻨﺔ : ﻳﻘﻮﻝ ﺣﺒﻴﺒﻨﺎ
ﺍﻟﻤﺼﻄﻔﻰ- ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ - (ﻳﺎ ﺃﻳﻬﺎ ﺍﻟﻨﺎﺱ
ﺃﻓﺸﻮﺍ ﺍﻟﺴﻼﻡ، ﻭﺃﻃﻌﻤﻮﺍ ﺍﻟﻄﻌﺎﻡ، ﻭﺻﻠﻮﺍ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ،
ﻭﺻﻠﻮﺍ ﺑﺎﻟﻠﻴﻞ ﻭﺍﻟﻨﺎﺱ ﻧﻴﺎﻡ، ﺗﺪﺧﻠﻮﺍ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﺑﺴﻼﻡ )
ﺭﻭﺍﻩ ﺃﺣﻤﺪ ﻭ ﺍﺑﻦ ﻣﺎﺟﺔ .
• ﺻﻠﺔ ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﺗﻨﺸﺮ ﺍﻟﺤﺐ ﻭﺍﻷﺧﻮﺓ : ﻻﺷﻚ ﺃﻥ
ﺍﻟﺘﻮﺍﺻﻞ ﻭﺻﻠﺔ ﺍﻟﺮﺣﻢ ﺳﺒﺐ ﻭﻋﺎﻣﻞ ﺃﺳﺎﺳﻲ ﻟﻨﺸﺮ
ﺍﻟﺤﺐ ﻭﺍﻟﻤﻮﺩﺓ ﺑﻴﻦ ﻛﻞ ﺃﻓﺮﺍﺩ ﺍﻟﻌﺎﺋﻠﺔ .
ﺑﺠﺎﻧﺐ ﻣﺎ ﺳﺒﻖ ﻓﺈﻥ ﺣﻴﺎﺗﻨﺎ ﻣﻠﻴﺌﺔ ﺑﻜﺜﻴﺮ ﻣﻦ ﺍﻟﺼﻌﺎﺏ
ﻭﺍﻟﻤﺸﺎﻛﻞ ﻭﻻﺑﺪ ﺃﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﻟﻨﺎ ﺃﻧﺲ ﻭﻋﺎﺋﻠﺔ ﻧﺴﻌﺪ ﺑﻬﺎ
ﻧﺸﻌﺮ ﻣﻌﻬﺎ ﺑﺎﻟﺮﺍﺣﺔ ﻭﺍﻻﺭﺗﻴﺎﺡ، ﻓﻀﻼً ﻋﻦ ﺃﻥ ﺻﻠﺔ
ﺍﻷﺭﺣﺎﻡ ﺗﻐﻔﺮ ﺍﻟﺬﻧﻮﺏ ﻭﺗﻘﺮﺑﻨﺎ ﻣﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﺰﻭﺟﻞ ﻟﺬﺍ
ﻓﺎﺣﺮﺻﻮﺍ ﻋﻠﻰ ﺻﻠﺔ ﺍﻟﺮﺣﻢ ﺩﺍﺋﻤﺎً