Ghadeer Khum 2
BIKIN
IDIN GHADIR KHUM KO GHADAR KHUM (Ranar bikin Idin Yaudara/Ranar bikin
Idin sanar da kafuwar Addinin Zagin Sahabbai) 18th/DHUL HIJJAH (2)
Bismillahi, wassalatu wassalamu ala Rasulillah, wa ala Alihi wa Ashabihi
Ajma'een. A shari'ar da Manzon Allah (saw) yazo da shi daga wurin
Allah Ta'alah, akwai kebantattun ranakun bukukuwan Idi guda uku (3)
wadanda bassu da na hudu. Wadannan shar'antattun idi na Musulunci sune :
1. IDIN BABBAN SALLAH (sallahr lahiya) 2. IDIN KARAMAR SALLAH (karamar
sallah) 3. IDIN SATI (ranar Jumu'a) Iyakan bukukuwan IDI kenan da
Addinin Musulunci ya sani, basu da na hudunsa. Saboda haka, duk wani
IDI bayan wadannan ukun, toh lallai bakon haure ne ba Idin Addinin
Musulunci bane, don haka zaka ga duk cikin littafan fiqhun Addinin
Musulunci sune ake kawo su da hukunce hukuncensu kamar ; wajibcinsu,
mustahabbansu, ladubbansu, dss. Sabanin wadannan zaka babu shi
ballantana hukunce hukuncen da ya kebantau da su. Shar'antuwar wadannan
idi guda uku sunzo da nassoshi kamar haka : (1-2). BABBA DA KARAMAR
SALLAH (Sallahr Lahiya) : ﻋﻦ ﺃﻧﺲ ﺽ ﻗﺎﻝ : ﻗﺪﻡ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺹ ﻭﻷﻫﻞ ﺍﻟﻤﺪﻳﻨﺔ ﻳﻮﻣﺎﻥ
ﻳﻠﻌﺒﻮﻥ ﻓﻴﻬﻤﺎ ﻓﻰ ﺍﻟﺠﺎﻫﻠﻴﺔ، ﻓﻘﺎﻝ : ﻗﺪﻣﺖ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻭﻟﻜﻢ ﻳﻮﻣﺎﻥ ﺗﻠﻌﺒﻮﻥ ﻓﺒﻬﻤﺎ ﻓﻰ
ﺍﻟﺠﺎﻫﻠﻴﺔ، ﻭﻗﺪ ﺃﺑﺪﻟﻜﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﻬﻤﺎ ﺧﻴﺮﺍ ﻣﻨﻬﻤﺎ : ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻨﺤﺮ ﻭﻳﻮﻡ ﺍﻟﻔﻄﺮ . "
ﺃﺧﺮﺟﻪ ﺃﺑﻮ ﺩﺍﻭﺩ )١١٣٤ ) "Daga Anas bn Malik r.a yace : Annabi s.a.w ya
taho (madina) alhali mutanen Madina suna da wasu ranaku biyu a
jahiliyya da suke wasanni a cikinsu, sai Yace : Na taho gareku kuna da
ranaku biyu da kuke wasanni cikinsu a jahiliyya, hakika Allah ya
musanya muku su da wasu biyun mafiya alheri da su : ranar idin yanka da
ranar idin karamar sallah." (3). IDIN SATI (Ranar Jumu'a) : Daga Anas
bn Malik (raa) yace, Annabi (saw) yace : ﺃﺗﺎﻧﻲ ﺟﺒﺮﻳﻞ ﺑﻤﺜﻞ ﺍﻟﻤﺮﺁﺓ
ﺍﻟﺒﻴﻀﺎﺀ، ﻓﻴﻬﺎ ﻧﻜﺘﺔ ﺳﻮﺩﺍﺀ، ﻗﻠﺖ : ﻳﺎ ﺟﺒﺮﻳﻞ، ﻣﺎ ﻫﺬﻩ؟ ﻗﺎﻝ : ﻫﺬﻩ ﺍﻟﺠﻤﻌﺔ،
ﺟﻌﻠﻬﺎ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻴﺪﺍ ﻟﻚ ﻭﻷﻣﺘﻚ ..... ﺍﻟﺦ ﺭﻭﺍﻩ ﺃﺑﻮ ﻳﻌﻠﻰ ) ٤٢١٣( ﻭﻏﻴﺮﻩ ﺑﺴﻨﺪ ﺣﺴﻦ .
"Annabi s.a.w yace : Jibrilu yazo min da kwatankwacin gilashi fari, a
cikinsa akwai digo baqi, sai Nace : Ya Jibrilu, mecece wannan? Yace :
wannan itace Jumu'a, Allah ya sanyata IDI gareka da al'ummarka ...."
Wadannan sune kadai ranakun Idi na Musulunci, duk wani abu koma bayan
wannan ba shi asali a karantarwan Manzon Allah (saw), don haka ne yayin
da wani bayahude yazo wurin Khalifa Umar 'Dan Khattab (ra) yake
kokarin ya kwadaitar da Musulmai su riki ranar da Ayahr "Alyauma akmalTu
lakuum dinaakum..." wacce ta sauka a filin Arfah a matsayin ranar Idi,
sai Umar r.a ya nuna masa sun san wuri da ranar da Ayahr ta sauka, amma
musulmai bassu yin hakan. ﻋﻦ ﻃﺎﺭﻕ ﺑﻦ ﺷﻬﺎﺏ ﻗﺎﻝ : ﺟﺎﺀ ﺭﺟﻞ ﻣﻦ ﺍﻟﻴﻬﻮﺩ ﺇﻟﻰ
ﻋﻤﺮ ﺑﻦ ﺍﻟﺨﻄﺎﺏ ﻓﻘﺎﻝ ﻟﻪ : ﻳﺎ ﺃﻣﻴﺮ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ، ﺁﻳﺔ ﻓﻰ ﻛﺘﺎﺑﻜﻢ ﺗﻘﺮﺀﻭﻧﻬﺎ، ﻟﻮ
ﻋﻠﻴﻨﺎ ﻣﻌﺸﺮ ﺍﻟﻴﻬﻮﺩ ﻧﺰﻟﺖ ﻻﺗﺨﺬﻧﺎ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﻋﻴﺪﺍ، ﻓﻘﺎﻝ : ﺃﻱ ﺁﻳﺔ؟ ﻗﺎﻝ :
>> ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺃﻛﻤﻠﺖ ﻟﻜﻢ ﺩﻳﻨﻜﻢ ﻭﺃﺗﻤﻤﺖ ﻋﻠﻴﻜﻢ ﻧﻌﻤﺘﻲ ﻭﺭﺿﻴﺖ ﻟﻜﻢ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﺩﻳﻨﺎ
No comments:
Post a Comment