Sunday 25 September 2016

HANA KARUWANCI DA FATAUCIN MIYAGUN KWAYOYI A Karamar Hukumar Kafur



 HANA KARUWANCI DA FATAUCIN MIYAGUN KWAYOYI  A Karamar Hukumar Kafur

Daga Hassan Kabir Yar'adua



HARAMTA KARUWANCI DA KULLE GIDAJEN GIYA/KAYAN MAYE 


A wata zantawa da nayi ta wayar tarho da kantoman riko na karamar Hukumar Kafur a jahar Katsina Alh Hamza Umar Nasarawa (Mai Garin Sabuwar Kasa) ya bayyana cewa sakamakon zaman da kwamitin tsaro na hukumar tayi kan korafi da aka yi game da lalacewar tarbiyyar matasa wanda karuwanci da gidajen giya/kayan maye ke haifarwa hakan yasa mu ka ga babu mafita illa muyi abunda Allah ya umarce mu (masu madafun iko) muyi na hana karuwancin da fataucin miyagun kwayoyin.
Shugaban karamar hukumar ya bayyana cewa sun sanya dokar kulle gidajen karuwanci da sha da fataucin kwayoyi a gaba dayan yankin na Kafur, duk wanda aka samu yana saidawa ko sha ko zuwa gidajen karuwancin to Doka za ta hau kanshi. Daga karshe ya bayyana cewa an rufe gidajen nan da ake masha’a.
                Wannan alkairin na da nasaba da canjin aiki da aikawa wani malamin addinin musulunci daga karamar hukumar Katsina zuwa Karamar hukumar Kafur, wanda ya bada gudumuwa kwaran gaske wurin tabbatar da wannan aikin alkhairin. Malamin yanzun haka yana ta kokarin sanya al’ummar yanki bisa koyarwar addinin musulunci ta hanyar gabatar masu da majalisai na karatu da kuma kokarin tabbatar da da’ar ma’aikatan yankin.
Muna fatan sauran kananan hukumomi da jahohi su ma su yi koyi da wannan karamar hukumar domin dorewar rayuwa ingantaciyya ta musulunci. 



No comments:

Post a Comment