Sunday 30 October 2016

Abubuwan Da Yariman Saudiya Yayi Kafin Rataye shi

Abubuwan Da Yariman Saudiya  Yayi Kafin  Rataye Shi-- Darasi Ga Kowa

Ismai'l Karatu Abdullahi

Kasar Saudiya, kasacewarta ta yi ƙaurin suna a duniya kan gudanar da hukuncinta kan gaskiya ga duk wanda ya aikata abunda bai dace ba, tana hukunci ne daidai da abunda ya aikata. Kutunan Saudiya masu adalci ne, basu bambamtawa wajen zartar da hukunci.

Wani abun misali ya faru a ranar 18 ga watan Oktoban shekara ta 2016,  inda aka rataye wani basarake ta dalilin kashe wani ɗan Saudiya mazauni ƙasar.

Yariman mai suna Turki Bin Saud Bin Turki Bin Saud Al Kabeer, an rataye shi. An yi masa haka ne daidai da abunda ya aikata kamar yadda dokan ƙasarsu ya kasance.

Yariman, mintuna kaɗan kafin a rataye shi, yayi wasu abubuwa  waɗanda za su kasance darasi a gare mu.

Ga kamar yadda ya yi: An Kashe Saud Bin Turki ne bisa kisan gilla da yayi wa wani- Adalci ga Kowa.

Mintuna kaɗan kafin rataye shi, ya nemi a bar shi ya gana da iyalanshi, kuma ya samu. Ya ɗauki kimanin awanni 4 tare da iyayensa da danginsa,  ba sai an yi bayanin abunda ya gudana ba kowa zai iya sani kamar yin ban kwana, ƙarfafa masa zunciya da neman gafara.

Daga bisani sai Limamin Masallacin Al Safa ya ce a ɗauko shi daga ganawar da iyalinsa waɗanda suka ta kiran sunanshi suna bankwana , babu abunda za ta ji sai kuka da alamun baƙin ciki. 

Muhammad Al Maslookhi ne ya watsa a shafinsa na "Twitter", Su kuma Shafin Saudi "News site Al Marsad", suka ruwaito.

Masu rataya suka ɗauke shi zuwa ofishin 'yan sanda inda nan ne zai rubuta wasiyarsa ta ƙarshe, amma bai iya rubutawa ba.

Da misalin karfe 11 na safe, iyalan wanda  Yariman ya kashe, suka iso inda aka sanar da su za a rataye ahi.

Yariman, yayi alwala, sannan ya jira lokacin da za a rataye shi.

Babba wansa, yayi ƙoƙarin magana da iyalin wanda  Yariman ya kashe   domin nema wa ƙaninsa gafara, da kuma ko zasu karɓi diyya, a yinkuri na karshe kafin a rataye Yariman amma sun ƙi yarda.

Bayan sallar Azahar, 'yan'uwan Yariman suka sake neman wannan alfarman daga iyayen waɗanda aka kashe amma sun ƙi amincewa.
    
Kamar yadda kuka sani musulunci ba addini ba ne mai danne hakkin kowa ba. Kamar yadda 'yan'uwan Yarima suka nemi iyalan wanda Yarima ya kashe da su karɓi diyya amma suka ƙi, don haka dole a zartar wa Yariman hukunci daidai da abunda ya aikata.

Yarima yayi sallar Azahar da La'asar. Bayan nan da karfe 4:13  aka rataye shi. Har aka rataye shi, babu abinda ya ke fitowa daga bakinshi sai karatun Alkur'ani da ambaton neman yafiya ga Allah.

Kar ku manta, an rataye Yariman ne sakamakon kashe wani da yayi da bindiga.

Addu'armu Allah Ya gafarta wa wanda aka kashe da shi da yayi kashin.

©Zuma Times Hausa

No comments:

Post a Comment