Thursday 13 October 2016

MALAMI DA DALIBINSA

*MALAMI DA DALIBINSA*

DALIBI:  Ya Sayyadi wace irin falala zamu samu Idan mu ka tada hatsaniya a cikin garuruwan mu Amman da sunan Muzaharar Ashura
MALAMI: Ai kuwa kuna da lada sosai ashe ba ku ganin yadda aka zubar da jinin Imam Husain
DALIBI: To MALAM shi Imam Husain ance mutanen Kufa ne su ka yaudare shi sukai ta kiransa yazo za su yi mai Mubaya'a karshe ya fito su ka sumbule su ka bari aka kashe shi.
MALAMI: Tabbas muna da ruwayoyi irin haka
DALIBI: Ko shi yasa na ga kamar da ruwayoyin su Sayyid da ku Amirai ku ke aiki
MALAMI: Ban gane ba
DALIBI: Eh to ai na ga mu Mabiya kullum mu ake kashewa ku kuma kullum sai dai ku ce mana za mu dau fansa za mu ga bayan Azzalumai,   kuma sai ku   yi ta ingaza mu ku na labewa
MALAMI: Wannan Ai tunanin Wahhabiyawa ne

DALIBI: Madalla da tunanin da bai jefa mabiyansa halaka ba
MALAMI: To mu dai soyayyar mu Husain ta sa mu ke haka
DALIBI: Amman Malam ka karata mana a Tafsirin Suratul Bakara cewa Allah ya ce " Kar ku jefa kan ku ga halaka" to Wannan ai shi ne misalin jefa kai ga halaka
MALAMI: An ya ba ka tasirantu da Wahabiyawan Fcbk ba don na ga kwanan husuma kawai kake nema
DALIBI: Haba Malam da ga na fadi gaskiya ni duk inda gaskiya ta ke ina nan
MALAMI: To ai kuwa sai dai in ka bar tunani irin na wahabiyawa, ka ga ai murna su ke gwamnati ta hana mu addinin mu
DALIBI: Yo MALAM an hana mu Yin Sallah ne ko wani rukuni daga rukunan Musulunci?
MALAMI: Mu fa addinin mu yana tafiya ne da a bisa tsarin bin maraji'anci don haka muna yin bukukuwa Wanda ba wanda ya isa ya hana mu
DALIBI: Ko da ya saba ma dokar kasa Malam
MALAMI.: Mu fa ba wata hukuma sai ta Allah
DALIBI: Ai da Wannan ku ka rude mu Amman mun gani har Iran ba hukumar Allah su ke big ba don su ma suna da tsarin mulkin su Wanda ba na Allah ba
MALAMI: Yanzun dai mu jajanta ma Juna kan Wannan zalunci da akai mana
DALIBI: Ai ni sai dai a taya ni murna ta barin Wannan tafiyar ta rashin sanin kimar Mabiya  (Shi'a)

No comments:

Post a Comment