Tuesday 25 October 2016

Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahad Husaini (R.A) (2)

  

 Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahada                            Husaini (R.A) (2)


Dr.Muhd Sani R/Lemu


‘Yan uwana masu karatu, kamar yadda na yi
muku alkawari a baya cewa, zan tsakuro muku
wani abu mai kama da taɓa-ka-lashe daga
cikin rubutun babban marubucin nan Ash-
Sheikh Ali at-Tantawi da ya rubuta ƙarkashin
waccen matashiya ta sama, a littafinsa mai
suna “Az-Zikrayaat” wato ‘Tuna Baya’. Ka da
ku manta na faɗa muku cewa, ba zan iya kawo
rubutunsa yadda yake ba, cike da fasaharsa da
taswirarsa, sai dai in kwatanta, domin an ce,
‘linzami ya fi ƙarfin bakin kaza’.
Malam dai ɗan asalin ƙasar Syria ne, amma ya
yi zaman karatu a Masar, sannan ya koyar a
Iraƙi, ya ziyarci wasu ƙasashe dadama, daga
ƙarshe ya yada zango a ƙasar Saudiya, a nan
Allah ya yi masa rasuwa a shekarar (1999
A.D). A zamansa a Bagadaza ta ƙasar Iraƙi ya
fita wata rana inda ya ga ‘mutuwa’ amma Allah
ya kuɓutar da shi, daga baya ya yi rubutu a
kan wannan labari, inda yake cewa,
“Ranar Ashura a Iraƙi wata rana ce ta daban.
Duk garin yakan koma tamkar ana zaman
makoki, kai ka ce, jiya-jiyan nan ne aka kashe
Husaini (r), ko kuma ka ce har yanzu Banu
Umayya ne ke rike da ragamar mulki; ko kuma
wadanda aka kashe Sayyidina Husaini (r) tare
da su, su ne a kan kujerar mulki. Mutane sun
manta da cewa, Duniyar fa ta canza, wasu
ƙasashe sun gushe, wasu kuma sun kafu,
komai a doron ƙasa ya canza akan yadda da
yake, kaɗai al’adar waɗannan mutane ne ita ce
ba ta canza ba har yanzu, jiya-a-yau.
Mu Musulmi duka muna son Annabi (S.A.W),
duk wanda ma ba ya son shi fiye da yadda
yake son kansa to imaninsa bai cika ba. Kuma
muna son duk mai son Manzon Allah (S.A.W).
Kuma jikokinsa Hasan da Husaini suna son shi,
don haka mu ma muna sonsu, muna son iyalan
gidan Manzon Allah duka, don haka ne ma
muke sa su a cikin salatin da muke yi wa
Annabi (S.A.W). Amma duk da haka ba za mu
taɓa yarda mu aikata abin da Annabi bai yi
umarni da aikata shi ba, don kuwa ba za mu
saɓa masa ba mu riƙa yin gaban-kanmu. Abin
da muka ga wasu mutane a Iraƙi suna yi ya
saɓawa koyarwar Annabi (S.A.W) kuma ba zai
taɓa amincewa da haka ba.
A wannan rana ta Ashura Abokina Anwar ya
buƙaci mu tafi garin Hillah (yanki ne na ‘yan
shi’a a Iraƙi) yawon buɗe ido. Sai na yarda.
Kuma muka nemi wasu ɗalibanmu su uku su yi
mana rakiya. A cikinsu akwai wani basamuden
ɗalibi, idan na tsaya kusa da shi dakyar kaina
yakan gota kwankwasonsa kaɗan, wani lokaci
ma nakan tsokane shi in ce masa, wai kai ba
ka gamuwa da matsalar iskar shaƙa (Oxygen) a
sararin samaniya idan kana tsaye?!. Amma
kuma duk da haka yaro ne mai kirki, mai
kyawawan halaye, sunanshi Abdullahi Adi. Ka ji
sunan shi ma ‘Adi’ kamar sauron ɓurɓushin
Adawa mutanen Annabi Hudu. (A.S). Sauran
ɗaliban guda biyu, ɗayansu ɗan Sunna ne,
gudan kuma ɗan Shi’a ne.
Kashe Sayyidana Husaini wata mummunar
aika-aika ce, e, zan sake maimaitawa,
mummunar aika-aika ce, a fahimci hakan da
kyau. To fa amma da jimawa wasu mawaƙa da
marubuta Adabin larabawa sun yi ta ƙarin
gishiri mai yawa a wajen bayanin wannan
‘aika-aika’ domin sun mayar da ita wani fage
na sukuwar dawakan adabinsu, da sakin
linzamin waƙoƙinsu. Lalle kam sun yi sukuwa
yadda suke so, to amma fa sun lullube gaskiyar
al’amarin da ƙurar sukuwar dawakansu.
Waƙi’ar kashe Husaini, waƙi’a ce da ta faru tun
shekaru masu yawa da suka wuce. Marubuta
iri-iri, kama daga marubutan tarihi da mawaƙa
da marubutan adabi da al’adu kowa ya yi ta
rubutu a kai, kuma kowa yana zana irin tashi
taswirar yadda waƙi’ar ta kasance. Kusan babu
wani labari mai sanya idanu su rika kwararo da
hawaye da ba a faɓa ba a kai. Duk wani abu
da yake nuna zalunci da rashin imani da
ƙeƙashewar zuciya, da nuna rashin mutunci da
tumasanci, duk sai da aka tattaro su aka zuba
su a cikin labarin wannan waƙi’a. Kai yau da a
ce Miyagun mutanen na da aka yi a tarihi irin
su, Nero ko Genghis khan, ko ma yahudawan
da suka fi su sharri a yau irin su Begin da
Shamir, su ne ake ba da labarin an yi musu irin
abin da masu ba da labarin waƙi’ar Karbala
suke faɗa, to babu shakka sai ka tausaya
musu idan ka ji, sai ka jajanta musu a kai. To
kuma balle a faɗa maka cewa, duk wannan
abu ya faru ne ga ‘ya ‘yan Nana Fatima, jikokin.
Ma’aiki (S.A.W) yaya za ka ji a ranka?!
Wannan shi ne zai sa ka fahimci dalilin da ya
sa muke ganin abin da ake yi a ranar Ashura
game da Husaini irin wanda ba a yi wa Ali ko
Mazon Allah kwatankwacinsa, alhali kuwa sun
fi shi daraja nesa ba kusa ba.
Muna tsakar yawo a garin Hillah ne, sai muka
gan mu a wani babban fili an zageye shi da
katanga, da ƙofar shiga guda ɗaya a buɗe.
Sannan muka ji wani sautin rera waƙe mai cike
da tausayi yana fitowa daga cikin wannan
kango. Muna leƙawa sai kawai mu ga wasu
mutane a ciki zaune babu komai na tufafi a
jikisu in banda abin da suka rufe al’aurarsu
zuwa cibiyoyinsu. Sun bar ƙirajensu tsirara a
waje. A tsakiyarsu sai muka hango wani zaune
sanye da koren rawani (alamar shi Sayyid ne
Ahlul Baiti). Wannan mutum shi ne mai ba da
waƙen, sauran jama’ar dake zagaye da shi
sahu-sahu suna masa amshi.
Daga nan sai abokina Anwar ya tambaye ni
cewa, ko za mu shiga wannan kangon ne? Sai
na ce mu tambayi waɗannan ɗaliban domin su
ne ‘yan gari, su suka fi mu sanin ƙasarsu. Sai
suka ce mana kada mu yarda mu shiga. Ai
kafin mu ankara shi gogan naka Anwar har ya
shige. Daga nan muma muka yanke shawarar
mu bi bayansa.
Mu kwana a nan, za mu ci gaba….

No comments:

Post a Comment