Monday 24 October 2016

KARATUN HAUZA DAGA MAJALISIN MAL BABAN HAMDAN


MAJALISI NA [ 1 ] na Sheikh Baban Hamdan


GAMUWA A KAN SAHIHIYAR AQIDA, SHINE RABA-GARDAMA A TSAKANIN MUTANE, SHINE HADIN KAN MUSULMI. SABANIN HAKA, HADIN-BAKI NE DA YAUDARAR JUNA.

MUTUM ZAI ZAMA MUSULMI NE KADAI, IDAN YA QUDURCI:

(1) BA ABIN BAUTA SAI ALLAH SHI KADAI, YA SHAIDA DA MANZANCIN ANNABI MUHAMMAD S.A.A.W.
(2) YA TSAIDA SALLAH
(3) YA AZUMCI WATAN RAMALANA
(4) YA BADA ZAKKA
(5) YAYI AIKIN HAJJI IDAN YA SAMI IKO.

IMANI, SAHIHIYAR AQIDA: SHAIKH SALIHUL FAUZAN, YACE:

وقد بقي النبي صلى الله عليه وسلم في مكة بعد البعثة ثلاثة عشر عامًا يدعو الناس إلى التوحيد، وإصلاح العقيدة؛ لأنها الأساسُ الذي يقوم عليه بناءُ الدين

"TUN DA AKA AIKO SHI, ANNABI S.A.W. YANA MAKKA SHEKARU 13 YANA KIRAN MUTANE ZUWA TAUHIDI DA GYARAN AQIDA, DOMIN ITACE ASASIN DA AKE GINA ADDINI AKAN TA"

A CIKIN LITTAFIN SA "AQIDATUT TAUHID" SHEHI YACE, SAHIHIYAR AQIDA ITACE:

الإيمان بالله وملائكته وكتبه ورسله واليوم الآخر، والإيمان بالقدر خيره وشره، وتُسمَّى هذه أركانُ الإيمان.

"IMANI DA ALLAH, DA MALA'IKUN SA, DA LITTAFAN SA, DA MANZANNIN SA, DA RANAR LAHIRA, IMANI DA QADDARA; AL-KHAIRI DA SHARRIN TA. WADANNAN SU AKE KIRA RUKUNAN IMANI"

'YAN SHI'A, WADANNAN SUNYI MUKU? IDAN SUNYI MUKU, TO KO A CIKIN DAREN NA MA, ZAMU FARA DA KALLON YADDA MUKA QUDURCI WADANNAN RUKUNNAI, TARE DA SANIN MADOGARAR MU AKAN AQIDUN NAMU.

IDAN KUNA DA ABIN DA BAKWA SO A CIKI, KO KU KARA, TO SAIKU LISSAFA SU, SAI SHIGA JERIN ABABEN DA ZAMU TATTAUNA AKAN SU, DOMIN KOWA YA SAN ABIN DA BAI SANI BA, GWARGWADON HALI, YA FAHIMCI ABIN DA BAI FAHIMTA BA.

ALLAH S.W.T. YACE:

واعتصموا بحبل الله جميعاً ولا تفرقوا

BISMILLAH...

MAJALISI NA [2] na Sheikh Baban Hamdan

RUKUNAN DA MUKA GAMU AKAN SU A MAJALISI NA [2], SUNA NAN A QUR'ANI. WANNAN NE; A GANI NA والله أعلم ; YA SA BA MUYI SABANIN WANDA YA SAME SU, SHINE MUSULMI, MUMINI BA.

ANA HAKA NE, SAI MALAMIN SHI'A MAI "ASALUS-SHI'ATI WA USULUHA, 59" MUHAMMAD HUSSAIN KASHIFUL GIDA' YACE:

الشيعة الإمامية زادت ركناً خامساً وهو الاعتقاد بالإمامة

"SHI'A SUN QARA RUKUNI NA BIYAR SHINE QUDURIN IMAMA"

ZA A IYA CEWA RUKUNI NA 6 NE, BA NA BIYAR BA, KO MUCE SUN RAGE RUKUNI DAYA, SAI SUKA QARA DAYA, YA ZAMA NA BIYAR, DOMIN DAMA RUKUNAN DA MUKAYI ITTIFAQI A KANSU BIYAR NE.

KO YAYA DAI, LAMARI NE DA YA HAIFAR DA SABANI, MUSAMMAN BAYAN HUKUNTA WANDA BAI BADA GASKIYA DA SHI BA, KAMAR YA QARYATA MANZANNI NE, WATO DAI, YA FITA DAGA ISLAM.

A "TALKHISUS SHAFIY NA DUWSIY, 4/131" DUWSIN YA CE:

ودفع الإمامة كفر كما أن دفع النبوة كفر لأن الجهل بهما على حد واحد

"YADDA KORE ANNABTA YAKE KAFIRCI, KORE IMAMA MA KAFIRCI NE, HUKUNCIN DAUKE KAI DAGA GARE SU DAYA NE"

WATA MATSALAR ITA CE, MATSAYIN IMAM. HAKANE, DUK WANDA YA YARDA SHI MUSULMI NE, TOH FA, DOLE YA BADA GASKIYA DA DOKACIN ABIN DA ALLAH YAZO MASA DASHI. AMMA ZAI GA ANYI KUDU DA KARE, IDAN YAJI SABON ABU, DA BAI GAMSU ALLAH NE YA HUKUNTA SHI BA.

INA SON A FAHIMCI, GAMSUWA KO RASHIN TA, KAN ALLAH NE YA HUKUNTA IMAMA, DALILI NE DA WANI ZAI QUDURCE TA KO YAYI WATSI DA ITA. KENAN, HANYA DAYA DA ZA A WARWARE SABANIN, ITACE TATTAUNAWA CIKIN LUMANA, DON A GAMSAR DA KOWA "EY KO A'A" BISA KARANTARWAR AL-QUR'ANI.

IMAM KHUMAINIY, CIKIN "AL-HUKUMATUL ISLAMIYYA 52" YACE:

إن من ضرورات مذهبنا أن لأئمتنا مقاماً لا يبلغه ملك مقرب ولا نبي مرسل

"DOLE NE A MAZHABAR MU, A QUDURCI IMAMAN MU SUNA DA WANI MATSAYI DA DUK KUSANCIN MALA'IKA (DA ALLAH) KO WANI MANZO DA AKA TURO, BAI KAI SHI BA"

MUHAMMAD JAWAD MUGNIYA "TAFSIRIN KASHIF 1/197" YA CE:

إن قول الإمام نبياً كان أو وصياً هو قول الله

"LALLAI MAGANAR IMAMI; ANNABI KO WASIYYI; DAI-DAI TAKE DA MAGANAR ALLAH"

MUZAFFAR A "AQA'IDUL IMAMIYYA 70" YACE:

ونعتقد أن الإمام كالنبي

"MUN QUDURCI CEWA IMAMI KAMAR ANNABI NE"

BANBANCIN SU TA FUSKAR WAHAYI NE, KAMAR YADDA KASHIFUL GHIDA' YACE A SHAFI 59:

إن الإمام لا يوحى إليه كالنبي وإنما يتلقى الأحكام منه مع تسديد إلهي

"LALLAI IMAMI BA A YI MASA WAHAYI IRIN NA ANNABI, SHI YANA KARBAR HUKUNCE-HUKUNCE NE TA HANYAR RUHI DAGA ALLAH"

A LURA CEWA WANNAN RUKUNIN DA 'YAN SHI'A SUKA QARA, YA BAYU GA BUDE KOFAR WASU HUKUNCE-HUKUNCE DA IMAMI ZAI KARBO DAGA ALLAH, YA ISAR DASU GA MABIYAN SA.

ASHE BA MATSAYIN AKE JA DASHI BA, AMMA ANA SARA NE ANA DUBAN BAKIN GATARI! ALLAH S.W.T. YA CE:

اليوم أكملت لكم دينكم وأتممت عليكم نعمتي ورضيت لكم الإسلام دينا

"A YAU NA CIKA MUKU ADDININ KU, NA CIKA NI'IMA TA A GARE KU, KUMA NA YARJE MUKU MUSULUNCI A MATSAYIN ADDINI"

KENAN, IDAN WANI YAZO DA WASU HUKUNCE-HUKUNCE SABABBI, DOLE AYI TAKA-TSAN-TSAN, DON KAR A MANTA DA MAGANAR ALLAH, A QOQARIN BIYAYYA GA ALLAH.

A HANU DAYA, ALLAH YA YARJEWA MUTANE MUSULUNCIN DA MUKA FARA DA RUKUNAN SA, GABANIN QARIN RUKUNI NA BIYAR KO NA SHIDA, WATO IMAMA DA 'YAN SHI'A SUKAYI.

TO SAI ABIN YA ZAMA WANI IRI, GASHI MUN DAUKO TAFIYA TARE, TIRYAN-TIRYAN, KAMAR YADDA QUR'ANI YA NUSASH-SHE MU, SAI 'YAN SHI'A SUKA FUTO DA WADANNAN QARE-QAREN, KAMAR YADDA SHI MALAMIN SHI'A KASHIFUL GIDA' YA FADA.

KENAN IDAN ZAMU HADU A KAN QUR'ANI, SAI MU TSAYA GA MUSULUNCIN MUTUM KO KAFIRCIN SA, GWARGWADON RUKUNAN DA QUR'ANI YA TABBATAR.

ME KUKE GANI?

No comments:

Post a Comment