Tuesday 13 June 2017

Amsoshin Tambayoyin Musabaqar Alaye Da Sahabban Annabi (S.A.W)


 Amsoshin Tambayoyin Musabaqar Alaye Da Sahabban Annabi (S.A.W)

الإجابة النموذجية
1
قال ابن عباس yفي قوله تعالى(لِكُلٍّ جَعَلْنَا مِنكُمْ شِرْعَةً وَمِنْهَاجًا) قال هي :
سبيل وسنة

رأي واجتهاد      

حكم وأخلاق
2
قال الحسين بن علي y في قولهI (ثُمَّ جَعَلْنَاكَ عَلَىٰ شَرِيعَةٍ مِّنَ الْأَمْرِ فَاتَّبِعْهَا) قال هي :
السنة

الولاية

الشيوخ
3
قال ابن عباس y: (ما يأتي على الناس عام إلا وأحدثوا بدعة وأماتوا سنة حتى تحيا البدع وتموت السنن )  هذا يدل على :

تحذير الصحابة من البدع  

خوف الصحابة على السنة          
كل ما سبق
4
قال ابن عباس رضي الله عنهما في  قوله I(أَوْ يَلْبِسَكُمْ شِيَعًا ) هي :
الأهواء المختلفة                    

الحيرة والشك                

الحق والعدل              
5
ناظر عبد الله بن عباس yالخوارج وبين لهم الحق بالدليل والبرهان فرجع منهم إلى الحق ألفان . رواه النسائي والبيهقي ..  تدل هذه المناظرة على
حرص الصحابةy على هداية الناس

صحة منهج الخوارج

عدم الرجوع إلى الحق
6
في صحيح البخاري ، وسنن أبي داود: قال ................. لأبيه عليِّ بن أبي طالبt: أيُّ الناس خير بعد رسول الله rقال: أبو بكرt، قلت: ثم مَن؟ قال: ثم عمرt  .       من القائل ؟ :

الحسن بن عليt

الحسين بن عليt
محمد بن علي بن الحنفية رحمه الله
7
يتولون أزواج النبي rويترضون عنهن، ويعرفون لهن حقوقهن، ويؤمنون بأنهن أزواجه في الدنيا والآخرة .    الذين يعتقدون خلاف هذا الاعتقاد في أمهات المؤمنين هم :

أهل السنة والجماعة                
الرافضة

الخوارج
8
سئل هشام بن حسان وهو في الطواف ما كان الحسن tيقول في الإيمان ؟ قال : قول وعمل  .. هذا القول يوافق قول :

المرجئة

الخوارج
أهل السنة والجماعة
9
قال ابن عباسy: ما عندي من تفسير القرآن فهو عن علي بن أبي طالبt . (تفسير التسهيل لعلوم التنزيل لابن جزي).         يدل هذا القول على :
غزارة علم علي t

مخالفة ابن عباس لعلي y

جميع ماسبق
10
قال ابن عباس y : (تكفل الله لمن قـرأ القرآن وعمـل بما فيه أن لا يضـــل في الدنيا ولا يشــقى في الآخرة ) وقرأ قوله I : (فَإِمَّا يَأْتِيَنَّكُم مِّنِّي هُدًى فَمَنِ اتَّبَعَ هُدَايَ فَلَا يَضِلُّ وَلَا يَشْقَىٰ(123) وَمَنْ أَعْرَضَ عَن ذِكْرِي فَإِنَّ لَهُ مَعِيشَةً ضَنكًا )  يدل مثل هذا التوجيه على :
البدع نتيجة البعد عن القرآن والسنة

بعد أهل السنة والجماعة عن مصادر التلقي  

كل ما سبق


11
قال حذيفة بن اليمان t: يا معشر القراء استقيموا وخذوا طريق من كان قبلكم فو الله لئن اتبعتموهم لقد سبقتم سبقا بعيدا ، ولئن أخذتم يمينا وشمالا لقد ظللتم ضلالا بعيدا .  هذا الأثر المراد به اتباع طريقة ومنهج :
الصحابة y

الزعماء

القراء
12
(الْيَوْمَ أَكْمَلْتُ لَكُمْ دِينَكُمْ وَأَتْمَمْتُ عَلَيْكُمْ نِعْمَتِي وَرَضِيتُ لَكُمُ الْإِسْلَامَ دِينًا) قـــال ابن عباس y: أخبر الله نبيه والمؤمنين أنه قد أكمل لهم الإيمان ولا يحتاجون إلى زيادة أبدا .     يدل هذا على:

جهود الصحابة وآل البيتy في الذب عن منهج السنة

أن ما لم يكن حين نزول الوحي دينا فليس اليوم بدين
كل ما سبق 
13
قوله I)يوْمَ تَبْيَضُّ وُجُوهٌ وَتَسْوَدُّ وُجُوهٌ) فأما الذين ابيضت وجوههم : فأهل السنة والجماعة وأولو العلم ، وأما الذين اسودت وجوههم : فأهل البدع والضلالة ، هذا المعنى ورد عن :
عبد الله بن عباس t

أبوبكر الصديقt

عائشة رضي الله عنها  
14
قال عبدالله بن مسعود t" اتبعوا ولا تبتدعوا فقد كُفيتم "  يدلقوله tعلى :

وجوب اتباع منهج الكتاب والسنة

التحذير من البدع             
جميع ماسبق
15
حذر الحسن t من أهل الأهواء فقال " لا تجالسوا أهل الأهواء ولا تجادلوهم ولا تسمعوا منهم " ..مِن أهل الأهواء :

أهل السنة والجماعة
الرافضة

جميع ماسبق
16
عن أبي بن كعب tقال : ( عليكم بالسبيل والسنة فإنه ما على الأرض عبد على السبيل والسنة وذكر الرحمن ففاضت عيناه من خشية الله عز وجل فيعذبه ... )  يستفاد من هذا الأثر

آثار اتباع السنة

أن سبيل السنة هو سبيل النجاة
جميع ماسبق
17
قال الحسن t: (  لا يصح القول إلا بالعمل ولا يصح العمل إلا بنية ولا يصح قول وعمل ونية إلا بالسنة  )  يستفاد من هذا الأثر :

الاكتفاء بالنية

الاكتفاء بالعمل 
أهمية الاتباع للسنة  
18
قال عمر t وروي ذلك أيضا عن علي t: ( سيأتي أناس يجادلونكم فخذوهم بالسنن فإن أصحاب السنن أعلم بكتاب الله )   يستفاد من الأثر في :
منهجية  الرد على المخالف

النهي عن مجادلة أهل البدع

مخالفة عمر لعلي
19
روى البخاري حديث أبي هريرةt قال: قال رسول الله r ((ستكون فتن القاعد فيها خير من القائم، والقائم خير من الماشي، والماشي فيها خير من الساعي، من تشرف لها تستشرفه))يدل هذا الحديث على :

مواجهة الفتن والمشاركة فيها
اعتزال الفتن وعدم الخوض فيها

الحرص على الفتن والمشي إليها
20
قال الرسول rفي معرض حديثه :(فعليكم بسنتي وسنة الخلفاء الراشدين المهديين من بعدي ، عضوا عليها بالنواجذ وإياكم ومحدثات الأمور فإن كل بدعة ضلالة)     يدل هذا الحديث على :

فضل الخلفاء الراشدين

التحذير من المحدثات في الدين
كل ما سبق


Monday 29 May 2017

An sanya mashi qwaya a jikkarsa a qasa mai Tsarki

HATTARA JAMA'A MUSAMMAN MASU ZUWA KASA MAI TSARKI (SAUDIYA), WASU NA SANYA
WA WASU MIYAGUN KWAYOYI A CIKIN KAYANSU!!!
A Kasar Musulunci ta Saudiya duk wanda aka
kama tare da miyagun kwayoyi suna aiwatar da
hukunci mai tsanani akansa wanda cikin ikon
Allah hakan da suke yi ya rage yawan mabarnata
a fadin kasar.
A cikin yan kwanakin nan wani bawan Allah dan
kasuwa dan jihar Kano ya tafi Kasa mai Tsarki
don yin Umrah shi da iyalinsa ashe wani azzalumi
daga nan ya sanya wa kayansa kullin tulin
kwayoyi shi kuma bai sani ba sai da ya kammala
aikinsa yana niyyar komowa gida ashe jami'an
tsaro tuni suna bibiyarsa har suka kama shi,
bawan Allahn gashi ya tabbatar da jikarsa ce
amma kuma baisan da ansa kwayar ba. Dan
uwansa yana gaya mani lallai suna da yaqinin
dan uwansu mutumin kirki ne wanda da wuya ya
aikata hakan, wannan bawan Allah yanzun haka
yana tsare ita kuma iyalinsa an maido ta gida.
Insha Allahu muna fata zaiyi nasara da wannan
zargi da ake masa kasancewar Kasar Saudia ba
azzaluma bace, Muna rokon Allah ya kare
wannan bawa nasa ya kuma tona asirin mutanen
da ke aikata wannan danyen aiki.
JAN HANKALI
Akwai barazana sosai kan irin wannan tunda
akwai mutanen da sun kware wurin shigar da
miyagun kwayoyi a kasar Saudia saboda haka ga
duk masu zuwa Umrah ko Aikin Hajji su sa ido ga
kayayyakinsu tun daga nan kasa Nigeria har
zuwa Kasar Saudiya.
Su ma Hukumominmu wajibi ne su kara
tsaurarawa don kaucewa faruwar irin wannan.
Ita kuma Kasa Mai Tsarki Allah yayi masu
jagoranci Amin

Saturday 27 May 2017

MURIDAN DARIQAR TIJANIYYA SUN QARA YIN TA'ADDANCI


Cikin masallacin kenan yadda suka maida shi
             Duk da haqilo da tunqahon da Mabiya dariqar Tijaniyya su ke yi na cewa sun fi kowa zaman lafiya da son zama lafiya wannan bai hana su afka ma al'ummar da ke masallacin Jan Bango kusada Hasumiya Katsina ba, bayan sun afkama masu su ka balle kwanon masallacin da tagoginsa haka kuma suka ciccire fankokin cikin masallacin sannan suka jikkata mutum uku.
Duk sun dauki wannan matakin ne a cewar su don daukar hukunci akan wai wani Malamin da ke karatu ya zagi Annabin mu Muhammad (S.A.W). Dr. Djibo Malami ne wanda yake karantar da sunnar Annabi Muhammad (S.A.W) a wannan unguwa wanda ya na cikin karatu ne a ranar Alhamis 25/05/17 tsakanin magriba da Isha'i inda anan ne suka rinqa afkowa suna zage-zage abun kamar wasa har suka fara amfani da makami inda anan ne suka raunata mutum uku ciki harda Dr.Djibo. Allah ya sa ka ma hukumar yan sanda da alheri don ana cikin hatsaniyar ne Allah ya kawo su su kai kokarin kwantar da tarzomar da kuma daukar daukar Malamin domin ba shi kariya don yunkurin muridan shine su hallaka shi da duk wani dan izalar da su ka ci karo da shi.
 Muna fatan hukuma ta dauki mataki na gagawa da hukunta duk wanda aka samu da laifi, haka kuma duk wadanada aka samu da laifin su gyara wannan masallaci domin irin wannan na uku kenan yana faruwa a yan shekarun nan don in ba a manta ba waccan shekarar haka a ka yi a masallacin Juma'a na Rafukka, muridan ne su ka zo su kai irin wannan ta'asa karshe aka zo akai ta sulhu da neman yafiya wanda a wannan karo al'umma sun ce ba za su yadda da hakan ba da fatan wannan koken zai isa inda ya dace. Allah ya hada kan musulmai.

Daga kasa hotunan irin wulakancin da muridan su kai ma dakin Allah ne.




                                               


Tuesday 16 May 2017

A TABBATAR DA TSARI NA SHAR’IAR MUSULUNCI DA KUMA KAFA HUKUMAR HISBA

A TABBATAR DA TSARI NA SHAR’IAR MUSULUNCI DA KUMA KAFA HUKUMAR HISBA
SAKO DAGA MATASAN MALAMAN JAHAR KATSINA
          A wa’azin da ya gabata ranar Asabar 13/05/2017, wanda Matasan Malaman su ka gabatar da wa’azi na karshe a cikin jerin wa’azuzukan da su ke gudanarwa duk bayan sati biyu, Wa’azin ya guda na ne a cibiyar baje kolin Sunnah wato masallacin Kandahar, inda gammayar malaman suka yi kira ga wannan gwamnatin cewa suna kira gareta da ta farfado da wannan tsarin wanda aka yi fafutikar tabbatar da shi a zamanin marigayi Malam Umaru Musa Yaradau. A kuma kafa hukumar Hisba a jihar domin yaqi da miyagun dabi’u mussamman zinace-zinace, fyade, shaye-shaye da sauransu.
Malam Zakariya’u Aliyu Sandamu (Limami na 2 a Masallacin gidan Gwamnati) ya yi kira da a dauki mataki don magance matsalar fyade inda ya bayyana cewa korafe-korafe sun yi yawa game da yi ma yara qanana fyade in da har ya bayyana yadda kwamishinan ‘yan sanda ya tabbatar cewa a cikin wannan shekarar an yi ma yara aqalla sama da 100 fyade. Wanda rahoto yazo masu, akwai da yawa ma wanda rahoton bai kai ga hukumar ba.
Haka nan kuma a wajen wa’azin an yi kira ga Gwamnati da ta duba yiwuwar maida makarantun kwana da aka kashe. Sannan kuma a duba yiwuwar  bada hutu a lokacin azumi don samun damar yin ibada yadda ya kamata.
Malaman da su ka gabatar da Wa’azin
1.     Malam Zakariya Aliyu Sandamu
2.     Mal Bunyaminu Muhd Balarabe
3.     Mal Safiyyu Alqasim
4.     Mal Abdur-rahim Sabi’u R/dadi
5.     Mal Abubakar Mai Kano
6.     Mal Haruna Sani Muhd
7.     Mal Aminu Usman
8.     Mal Munir Isah Kerau
9.     Mal Abdullahi Ayuba
10.                        Mal Shamsuden Abdul-Karim
11.                        Mal Muhd  Usamatu  
Hassan Kabir Yaradua
Ya ruwaito.

16/04/2017