A
TABBATAR DA TSARI NA SHAR’IAR MUSULUNCI DA KUMA KAFA HUKUMAR HISBA
SAKO
DAGA MATASAN MALAMAN JAHAR KATSINA
A wa’azin da ya
gabata ranar Asabar 13/05/2017, wanda Matasan Malaman su ka gabatar da wa’azi
na karshe a cikin jerin wa’azuzukan da su ke gudanarwa duk bayan sati biyu,
Wa’azin ya guda na ne a cibiyar baje kolin Sunnah wato masallacin Kandahar,
inda gammayar malaman suka yi kira ga wannan gwamnatin cewa suna kira gareta da
ta farfado da wannan tsarin wanda aka yi fafutikar tabbatar da shi a zamanin
marigayi Malam Umaru Musa Yaradau. A kuma kafa hukumar Hisba a jihar domin yaqi
da miyagun dabi’u mussamman zinace-zinace, fyade, shaye-shaye da sauransu.
Malam Zakariya’u Aliyu Sandamu (Limami na 2 a Masallacin gidan Gwamnati)
ya yi kira da a dauki mataki don magance matsalar fyade inda ya bayyana cewa
korafe-korafe sun yi yawa game da yi ma yara qanana fyade in da har ya bayyana
yadda kwamishinan ‘yan sanda ya tabbatar cewa a cikin wannan shekarar an yi ma
yara aqalla sama da 100 fyade. Wanda rahoto yazo masu, akwai da yawa ma wanda
rahoton bai kai ga hukumar ba.
Haka nan kuma a wajen wa’azin an yi kira ga Gwamnati da ta duba
yiwuwar maida makarantun kwana da aka kashe. Sannan kuma a duba yiwuwar bada hutu a lokacin azumi don samun damar yin
ibada yadda ya kamata.
Malaman da su ka gabatar da Wa’azin
1.
Malam Zakariya Aliyu Sandamu
2.
Mal Bunyaminu Muhd Balarabe
3.
Mal Safiyyu Alqasim
4.
Mal Abdur-rahim Sabi’u R/dadi
5.
Mal Abubakar Mai Kano
6.
Mal Haruna Sani Muhd
7.
Mal Aminu Usman
8.
Mal Munir Isah Kerau
9.
Mal Abdullahi Ayuba
10.
Mal Shamsuden Abdul-Karim
11.
Mal Muhd Usamatu
Hassan
Kabir Yaradua
Ya
ruwaito.
16/04/2017
No comments:
Post a Comment