Saturday 27 May 2017

MURIDAN DARIQAR TIJANIYYA SUN QARA YIN TA'ADDANCI


Cikin masallacin kenan yadda suka maida shi
             Duk da haqilo da tunqahon da Mabiya dariqar Tijaniyya su ke yi na cewa sun fi kowa zaman lafiya da son zama lafiya wannan bai hana su afka ma al'ummar da ke masallacin Jan Bango kusada Hasumiya Katsina ba, bayan sun afkama masu su ka balle kwanon masallacin da tagoginsa haka kuma suka ciccire fankokin cikin masallacin sannan suka jikkata mutum uku.
Duk sun dauki wannan matakin ne a cewar su don daukar hukunci akan wai wani Malamin da ke karatu ya zagi Annabin mu Muhammad (S.A.W). Dr. Djibo Malami ne wanda yake karantar da sunnar Annabi Muhammad (S.A.W) a wannan unguwa wanda ya na cikin karatu ne a ranar Alhamis 25/05/17 tsakanin magriba da Isha'i inda anan ne suka rinqa afkowa suna zage-zage abun kamar wasa har suka fara amfani da makami inda anan ne suka raunata mutum uku ciki harda Dr.Djibo. Allah ya sa ka ma hukumar yan sanda da alheri don ana cikin hatsaniyar ne Allah ya kawo su su kai kokarin kwantar da tarzomar da kuma daukar daukar Malamin domin ba shi kariya don yunkurin muridan shine su hallaka shi da duk wani dan izalar da su ka ci karo da shi.
 Muna fatan hukuma ta dauki mataki na gagawa da hukunta duk wanda aka samu da laifi, haka kuma duk wadanada aka samu da laifin su gyara wannan masallaci domin irin wannan na uku kenan yana faruwa a yan shekarun nan don in ba a manta ba waccan shekarar haka a ka yi a masallacin Juma'a na Rafukka, muridan ne su ka zo su kai irin wannan ta'asa karshe aka zo akai ta sulhu da neman yafiya wanda a wannan karo al'umma sun ce ba za su yadda da hakan ba da fatan wannan koken zai isa inda ya dace. Allah ya hada kan musulmai.

Daga kasa hotunan irin wulakancin da muridan su kai ma dakin Allah ne.




                                               


Tuesday 16 May 2017

A TABBATAR DA TSARI NA SHAR’IAR MUSULUNCI DA KUMA KAFA HUKUMAR HISBA

A TABBATAR DA TSARI NA SHAR’IAR MUSULUNCI DA KUMA KAFA HUKUMAR HISBA
SAKO DAGA MATASAN MALAMAN JAHAR KATSINA
          A wa’azin da ya gabata ranar Asabar 13/05/2017, wanda Matasan Malaman su ka gabatar da wa’azi na karshe a cikin jerin wa’azuzukan da su ke gudanarwa duk bayan sati biyu, Wa’azin ya guda na ne a cibiyar baje kolin Sunnah wato masallacin Kandahar, inda gammayar malaman suka yi kira ga wannan gwamnatin cewa suna kira gareta da ta farfado da wannan tsarin wanda aka yi fafutikar tabbatar da shi a zamanin marigayi Malam Umaru Musa Yaradau. A kuma kafa hukumar Hisba a jihar domin yaqi da miyagun dabi’u mussamman zinace-zinace, fyade, shaye-shaye da sauransu.
Malam Zakariya’u Aliyu Sandamu (Limami na 2 a Masallacin gidan Gwamnati) ya yi kira da a dauki mataki don magance matsalar fyade inda ya bayyana cewa korafe-korafe sun yi yawa game da yi ma yara qanana fyade in da har ya bayyana yadda kwamishinan ‘yan sanda ya tabbatar cewa a cikin wannan shekarar an yi ma yara aqalla sama da 100 fyade. Wanda rahoto yazo masu, akwai da yawa ma wanda rahoton bai kai ga hukumar ba.
Haka nan kuma a wajen wa’azin an yi kira ga Gwamnati da ta duba yiwuwar maida makarantun kwana da aka kashe. Sannan kuma a duba yiwuwar  bada hutu a lokacin azumi don samun damar yin ibada yadda ya kamata.
Malaman da su ka gabatar da Wa’azin
1.     Malam Zakariya Aliyu Sandamu
2.     Mal Bunyaminu Muhd Balarabe
3.     Mal Safiyyu Alqasim
4.     Mal Abdur-rahim Sabi’u R/dadi
5.     Mal Abubakar Mai Kano
6.     Mal Haruna Sani Muhd
7.     Mal Aminu Usman
8.     Mal Munir Isah Kerau
9.     Mal Abdullahi Ayuba
10.                        Mal Shamsuden Abdul-Karim
11.                        Mal Muhd  Usamatu  
Hassan Kabir Yaradua
Ya ruwaito.

16/04/2017

Thursday 27 April 2017

Koken al'ummar Garin Ketare ga Gwamnati

Sako zuwa ga mahukuntan Jihar Katsina
Daga al'ummar garin Ketare (karamar hukumar
Kankara)
Wani mummunan fasadi ake aikatawa tsawan
watani 3 a garin Ketare da wasu kauyuka a kusa
da shi, mutan garin sunyi bakin kokarin su amma
kasancewar tsageran sun samu goyon baya
kwaran gaske. Na samu wannan koken a satin
nan kuma na bincika na tabbatar da abubuwan
da koken ya kunsa.
Ga koken nan
"Assalamu ailaikum muna Mika koke da neman
taimako domin tada yan kungiyar gala/solo da
aka kawo mana a garin ketare Kuma aka yi masu
masauki a asibitin dake garin ketare kimanin
Wata hudu (4) kenan. Zuwan wadannan yan gala
ya haifar mana da matsaloli kamar haka. Lalata
tarbiya malali. 1. Irin abinda Ke faruwa a
Makarantar primary ta garin ketare Inda aka sami
yara maza da mata suna kwaikwayon irin abinda
yan kungiyar keyi Inda maza Ke hawan kan mata
har ma wani Yaron yana cewa Wata tazo Yayi
mata ciki Wannan ya ya faru Ranar 24/3/2017.
2. Kiran junansu da sunayen batsa irin na yan
kungiyar kamar irinsu kankana uwar ruwa da
sauran su..... 3. Barazanar tsaro wanda abaya
mun sami sauqi Amma yanzu kullum sai ansami
Inda akayi sata a garin
4. Keta haddi da bautar da kananan yara ,mafi
yawan yan matan da ake amfani dasu a wajan da
kadan suka wuce shekara goma . 5.bijirewar da
ya'ya' Ke yima iyayensu.
6. Barazana ta bangaren lapia tsoron yaduwar
cututtukan zamani. Dukkan su sunsabama
dokokin addinin musulunchi da Kuma dokokin
jihar katsina da Al adun muzauna garin
Mun gabatar da wadannan matsaloli a gaban
kwamitin tsaro na karamar hukumar Kankara
Ranar 6/04/2017 Inda kwamitin tsaron ya kasa
dakatar dasu saboda furucin da Magaji dogari
Yayi nacewar Idan aka tadasu to za ayi Bala'i
Inda yasami goyon bayan Staff Officer Kankara
Local Government lmrana dake da awar yana da
daurin gindi a wajan gwamna. Ta dalilin haka
kungiyar ta yadu a garuruwa kamar Ketare da
Burdugau da Kuma Sabon Layi Kuma Suna
samun kariya Daga yan sandan karamar hukumar
Kankara"
Wannan shine koken al'ummar wannan gari.
Akwai hotuna masu motsi na yadda wadanan yan
Galar suke kwana suna kade-kade mazansu da
matansu har gari ya waye.
Daga karshe muna kira ga gwamnatin wannan
jiha da ta dubi girman Allah da ta dau mataki na
gaugawa domin ceto al'ummar wannan yankin.
Haka kuma muna kira da babbar murya da
babbar murya ga wannan gwamnati da tayi
kokarin kafa kungiyar Hisba domin lura da irin
wadanan matsaltsalu.

Hussain Kabir Yaradua
27/04/17

Wednesday 5 April 2017

Jami'ar Al-Qalam ta tallafa ma yan gudun hijira a karo na biyu

Jami'ar musulunci ta Al-Qalam dake Katsina ta qara tallafa ma yan gudun hijira mazauna jihar ta Katsina a jiya Talata 04/04/17. Shugaban Jami'ar Prof Shehu Ado Garki ne ya hannanta kayan ga kungiyar mata masu da'awa wato Da'awah Family Support Katsina wanda ke kula da yan gudun hijirar, Shugaban jami'ar  ya bayyana cewa wannan shine karo na biyu da suka bada irin wannan tallafi,  kayayyakin da aka bada tallafin sun hada da Buhun masara guda 6, sai buhun gero guda 1, sai  buhun shinkafa guda 5, kwalin supergetti guda 7, Jarkokin mai guda 3.
A garin Katsina akwai yan gudun hijira wanda aqalla sun haura mutum 800 wanda qungiyar Da'awah Family Support ke kula da cin su da shansu, mazaunin su da suturarsu da kuma maganinsu DSS. duk wannan qungiya ke kula da su. Kamar yadda Malama Asiya shugaban kwamitin Idps ta kungiyar ta bayyana. Taron bada tallafin ya samu halartar mataimakin shugaban jami'ar Dr. Muhd Muslim Ibrahim, Rajistra, Bursar, Mustapha Audu Radda (P.R.O) da sauran muqaraban jami'ar, daga bangaren Da'awah Family support kuma Akwai Malama Asiya da kuma uwar kungiyar Da'awah Family Support Haj. Amina Ahmad Bawa Faskari, Husain Kabir Yaradua sai kuma Hasan Kabir Yaradua. Daga qarshe muna kira ga al'ummar jihar Katsina musamman masu hannu da shuni da su yi koyi da wannan jami'a wajan taimaka ma yan gudun hijira wanda Duke cikin wani irin mawuyacin hali wanda ta kai wasun su har sun fara bara. Allah ya agaza masu ya kuma bamu ikon taimakawa.

Hasan Kabir Yaradua

05/04/17.

Sunday 12 March 2017

Sheik Daurawa ya nemi gwamnatin Katsina da ta kafa hukumar Hisba a


Daurawa Ya Nemi Gwamnatin Katsina Ta Kafa Hisba A Jihar

Daga Hussain Kabir Yar'adua

Babban malamin Addinin musulunci kuma kwamandan Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya nemi gwamnatin jihar Katsina ta kafa hukumar Hisba a jihar.

Malamin wanda ya gabatar da Wa'azi a Masallacin Juma'a na Bani Kumasi wanda Kungiyar Muslim Ummah suka shirya a a yau asabar yayi kira ga Gwamnatin ne lura da yanda ake ta kai korafe korafen saki, yawan barace barace DSS. Malamin ya bayyana kokarin da gwamnatin tayi a baya dasu ka  gabata inda ya zanta dasu ya kuma basu shawarwari don kafuwar hukumar a jahar. Malam ya bayyana irin alkairan da za'a samu karkashin hukumar.

Wa'azin ya samu halartar manyan mutane daga jihar kamar su Tsohon sufetan Yan sanda Alh Ibrahim Ahmadu Kumasie, shugaban Kungiya Muslim Ummah Na Jihar Katsina Dr. Misbahu Na'iya, Mai Shari'a Musa Danladi, Alh Muh'd Sanusi Wada, Mal Haris Isah Dukke, Mal Samu Adamu Bakori.

Sunday 12 February 2017

Yada Hoton Gawa

Daga Malaminmu:

Dr. Muhd Sani Umar

Yada Hoton Gawar Dan Uwanka Mumuni Ba aiki Ne Na Masu Sanin Ya Kamata Ba

Wadanda suke dauko hutunan gawawwakin 'yan uwansa musulmi suna yadawa a dandalin sadarwa, wai don su sanar da rasuwarsu ko su yi ta'aziyyarsu, masu yin haka ba sa kyautawa ko kadan. Yin haka alama ce ta rashin wayewa da karancin fahimtar addini.

Gawar dan uwanka tana da alfarma da mutunci, bai kamata ka keta masa wannan mutuncin ba bayan mutuwarsa. Shi ya sa ko wankan gawa ba kowa ake sa wa ba sai wanda aka yarda da shi.

Ka duba, mutum ko barci yake yi ba zai so a dauki hotonsa ana yadawa ba, saboda ba lalle ne ya kasance cikin yanayin da zai so a gansa a cikinsa ba. Ka dubi yanayinka kai kanka, idan za a dauki hotonka kakan shirya don ganin hotonka ya yi kyawon kama, to don menene za ka rika baza hoton gawar dan uwanka bayan mutuwarsa? Kuma shin ba za a yarda da labarin mutuwarsa ba ne sai ka sa hotonsa?

Abin takaici ma wani lokaci wani ya jima da rasuwa amma idan wani ya zo magana a kansa sai ya sako gawarsa a cikin wani yanayi wanda bai dace ba sam, kuma shi mamacin da yana da rai ba zai so a gan shi a wannan yanayin ba.

Wani lokaci 'yan uwa za su yi hadarin mota suna kwance kace-kace cikin jini, sai wani sakarai ya dauko hotunansu yana bazawa wai shi a tunaninsa daidai yake yi, tir da irin wannan aiki na rashin nutsuwa.

Mu kiyaye hakkin yan uwanmu bayan mutuwarsu kamar yadda muke kiyaye shi a lokacin rayuwarsu. Allah ka ba mu kyakkyawar fahimta. Amin.

Sunday 5 February 2017

Rashin Lafiyar Buhari

Rashin lafiyar Buhari.

Daga Malam Baban Hamdan

Da farko dai Buhari mutum ne, bawan Allah, akwai rashin lafiya a kan sa akwai mutuwa, don haka in Buhari ya yi rashin lafiya ko ya mutu ba wani abu ne da ya sabawa al'ada ba.

Allah Ya wa Buhari ni'imomi da yawa da bai wa da yawan mutanen duniya ba. Yau ina shugabannin qasar da su ka yi mulki tare da Buhari a lokacin da ya shugabanci qasar nan a karon farko? Da yawa na sun mutu ba? Wasu tun tuni ba su da lafiya, wasu al'ummar qasar su ne su ka taru su ka kawar da su don ba sa son su, amma yau Buhari ba shi da lafiya duk wani mutumim azziki ya damu, har munafukan da su ke sukansa a baya sun gaggauta lashe amansu na sukansa da su ke yi.

To ku sani, kada rashin lafiyar Buhari ta tada muku hankali, kamar yadda Mallam Garba Shehu ya fada, Buhari ba cikin wani matsanancin yanayi ya ke ba, ko alama.

Ah, yo to ma idan kuna ganin abin da muke fada ba haka bane, ina hankulanku su ke? Ashe ba ku san rashin lafiyar ko wane shugaban qasa a duniyar nan babban labari ne ga manema labaran duniya ba? Shugaban Qasarku ne, amma a tunaninku kun fi kafafen yada labarai na qasa da qasa qishin ruwan son sanin halin da Buhari ya ke ciki da rawar qafar yadawa?

Balle Shugaban Qasa kamar Buhari, lamarinsa ya na maruqar daukan hankalin kafafen yada labaran qasa da qasa sabo da dalilai da yawa.

Ba na so in ja ku a wannan karon, amma insha Allah idan na sami zama zan dora daga inda na tsaya. Maganar dai ita ce kawai a ci gaba da yi wa Buhari addu'a, amma kowa ya kwantar da hankalinsa, insha Allah Buhari ya na tafe cikin nasara da Qarfin Mulkin Allah.