Thursday 27 April 2017

Koken al'ummar Garin Ketare ga Gwamnati

Sako zuwa ga mahukuntan Jihar Katsina
Daga al'ummar garin Ketare (karamar hukumar
Kankara)
Wani mummunan fasadi ake aikatawa tsawan
watani 3 a garin Ketare da wasu kauyuka a kusa
da shi, mutan garin sunyi bakin kokarin su amma
kasancewar tsageran sun samu goyon baya
kwaran gaske. Na samu wannan koken a satin
nan kuma na bincika na tabbatar da abubuwan
da koken ya kunsa.
Ga koken nan
"Assalamu ailaikum muna Mika koke da neman
taimako domin tada yan kungiyar gala/solo da
aka kawo mana a garin ketare Kuma aka yi masu
masauki a asibitin dake garin ketare kimanin
Wata hudu (4) kenan. Zuwan wadannan yan gala
ya haifar mana da matsaloli kamar haka. Lalata
tarbiya malali. 1. Irin abinda Ke faruwa a
Makarantar primary ta garin ketare Inda aka sami
yara maza da mata suna kwaikwayon irin abinda
yan kungiyar keyi Inda maza Ke hawan kan mata
har ma wani Yaron yana cewa Wata tazo Yayi
mata ciki Wannan ya ya faru Ranar 24/3/2017.
2. Kiran junansu da sunayen batsa irin na yan
kungiyar kamar irinsu kankana uwar ruwa da
sauran su..... 3. Barazanar tsaro wanda abaya
mun sami sauqi Amma yanzu kullum sai ansami
Inda akayi sata a garin
4. Keta haddi da bautar da kananan yara ,mafi
yawan yan matan da ake amfani dasu a wajan da
kadan suka wuce shekara goma . 5.bijirewar da
ya'ya' Ke yima iyayensu.
6. Barazana ta bangaren lapia tsoron yaduwar
cututtukan zamani. Dukkan su sunsabama
dokokin addinin musulunchi da Kuma dokokin
jihar katsina da Al adun muzauna garin
Mun gabatar da wadannan matsaloli a gaban
kwamitin tsaro na karamar hukumar Kankara
Ranar 6/04/2017 Inda kwamitin tsaron ya kasa
dakatar dasu saboda furucin da Magaji dogari
Yayi nacewar Idan aka tadasu to za ayi Bala'i
Inda yasami goyon bayan Staff Officer Kankara
Local Government lmrana dake da awar yana da
daurin gindi a wajan gwamna. Ta dalilin haka
kungiyar ta yadu a garuruwa kamar Ketare da
Burdugau da Kuma Sabon Layi Kuma Suna
samun kariya Daga yan sandan karamar hukumar
Kankara"
Wannan shine koken al'ummar wannan gari.
Akwai hotuna masu motsi na yadda wadanan yan
Galar suke kwana suna kade-kade mazansu da
matansu har gari ya waye.
Daga karshe muna kira ga gwamnatin wannan
jiha da ta dubi girman Allah da ta dau mataki na
gaugawa domin ceto al'ummar wannan yankin.
Haka kuma muna kira da babbar murya da
babbar murya ga wannan gwamnati da tayi
kokarin kafa kungiyar Hisba domin lura da irin
wadanan matsaltsalu.

Hussain Kabir Yaradua
27/04/17

Wednesday 5 April 2017

Jami'ar Al-Qalam ta tallafa ma yan gudun hijira a karo na biyu

Jami'ar musulunci ta Al-Qalam dake Katsina ta qara tallafa ma yan gudun hijira mazauna jihar ta Katsina a jiya Talata 04/04/17. Shugaban Jami'ar Prof Shehu Ado Garki ne ya hannanta kayan ga kungiyar mata masu da'awa wato Da'awah Family Support Katsina wanda ke kula da yan gudun hijirar, Shugaban jami'ar  ya bayyana cewa wannan shine karo na biyu da suka bada irin wannan tallafi,  kayayyakin da aka bada tallafin sun hada da Buhun masara guda 6, sai buhun gero guda 1, sai  buhun shinkafa guda 5, kwalin supergetti guda 7, Jarkokin mai guda 3.
A garin Katsina akwai yan gudun hijira wanda aqalla sun haura mutum 800 wanda qungiyar Da'awah Family Support ke kula da cin su da shansu, mazaunin su da suturarsu da kuma maganinsu DSS. duk wannan qungiya ke kula da su. Kamar yadda Malama Asiya shugaban kwamitin Idps ta kungiyar ta bayyana. Taron bada tallafin ya samu halartar mataimakin shugaban jami'ar Dr. Muhd Muslim Ibrahim, Rajistra, Bursar, Mustapha Audu Radda (P.R.O) da sauran muqaraban jami'ar, daga bangaren Da'awah Family support kuma Akwai Malama Asiya da kuma uwar kungiyar Da'awah Family Support Haj. Amina Ahmad Bawa Faskari, Husain Kabir Yaradua sai kuma Hasan Kabir Yaradua. Daga qarshe muna kira ga al'ummar jihar Katsina musamman masu hannu da shuni da su yi koyi da wannan jami'a wajan taimaka ma yan gudun hijira wanda Duke cikin wani irin mawuyacin hali wanda ta kai wasun su har sun fara bara. Allah ya agaza masu ya kuma bamu ikon taimakawa.

Hasan Kabir Yaradua

05/04/17.

Sunday 12 March 2017

Sheik Daurawa ya nemi gwamnatin Katsina da ta kafa hukumar Hisba a


Daurawa Ya Nemi Gwamnatin Katsina Ta Kafa Hisba A Jihar

Daga Hussain Kabir Yar'adua

Babban malamin Addinin musulunci kuma kwamandan Hisba, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya nemi gwamnatin jihar Katsina ta kafa hukumar Hisba a jihar.

Malamin wanda ya gabatar da Wa'azi a Masallacin Juma'a na Bani Kumasi wanda Kungiyar Muslim Ummah suka shirya a a yau asabar yayi kira ga Gwamnatin ne lura da yanda ake ta kai korafe korafen saki, yawan barace barace DSS. Malamin ya bayyana kokarin da gwamnatin tayi a baya dasu ka  gabata inda ya zanta dasu ya kuma basu shawarwari don kafuwar hukumar a jahar. Malam ya bayyana irin alkairan da za'a samu karkashin hukumar.

Wa'azin ya samu halartar manyan mutane daga jihar kamar su Tsohon sufetan Yan sanda Alh Ibrahim Ahmadu Kumasie, shugaban Kungiya Muslim Ummah Na Jihar Katsina Dr. Misbahu Na'iya, Mai Shari'a Musa Danladi, Alh Muh'd Sanusi Wada, Mal Haris Isah Dukke, Mal Samu Adamu Bakori.

Sunday 12 February 2017

Yada Hoton Gawa

Daga Malaminmu:

Dr. Muhd Sani Umar

Yada Hoton Gawar Dan Uwanka Mumuni Ba aiki Ne Na Masu Sanin Ya Kamata Ba

Wadanda suke dauko hutunan gawawwakin 'yan uwansa musulmi suna yadawa a dandalin sadarwa, wai don su sanar da rasuwarsu ko su yi ta'aziyyarsu, masu yin haka ba sa kyautawa ko kadan. Yin haka alama ce ta rashin wayewa da karancin fahimtar addini.

Gawar dan uwanka tana da alfarma da mutunci, bai kamata ka keta masa wannan mutuncin ba bayan mutuwarsa. Shi ya sa ko wankan gawa ba kowa ake sa wa ba sai wanda aka yarda da shi.

Ka duba, mutum ko barci yake yi ba zai so a dauki hotonsa ana yadawa ba, saboda ba lalle ne ya kasance cikin yanayin da zai so a gansa a cikinsa ba. Ka dubi yanayinka kai kanka, idan za a dauki hotonka kakan shirya don ganin hotonka ya yi kyawon kama, to don menene za ka rika baza hoton gawar dan uwanka bayan mutuwarsa? Kuma shin ba za a yarda da labarin mutuwarsa ba ne sai ka sa hotonsa?

Abin takaici ma wani lokaci wani ya jima da rasuwa amma idan wani ya zo magana a kansa sai ya sako gawarsa a cikin wani yanayi wanda bai dace ba sam, kuma shi mamacin da yana da rai ba zai so a gan shi a wannan yanayin ba.

Wani lokaci 'yan uwa za su yi hadarin mota suna kwance kace-kace cikin jini, sai wani sakarai ya dauko hotunansu yana bazawa wai shi a tunaninsa daidai yake yi, tir da irin wannan aiki na rashin nutsuwa.

Mu kiyaye hakkin yan uwanmu bayan mutuwarsu kamar yadda muke kiyaye shi a lokacin rayuwarsu. Allah ka ba mu kyakkyawar fahimta. Amin.

Sunday 5 February 2017

Rashin Lafiyar Buhari

Rashin lafiyar Buhari.

Daga Malam Baban Hamdan

Da farko dai Buhari mutum ne, bawan Allah, akwai rashin lafiya a kan sa akwai mutuwa, don haka in Buhari ya yi rashin lafiya ko ya mutu ba wani abu ne da ya sabawa al'ada ba.

Allah Ya wa Buhari ni'imomi da yawa da bai wa da yawan mutanen duniya ba. Yau ina shugabannin qasar da su ka yi mulki tare da Buhari a lokacin da ya shugabanci qasar nan a karon farko? Da yawa na sun mutu ba? Wasu tun tuni ba su da lafiya, wasu al'ummar qasar su ne su ka taru su ka kawar da su don ba sa son su, amma yau Buhari ba shi da lafiya duk wani mutumim azziki ya damu, har munafukan da su ke sukansa a baya sun gaggauta lashe amansu na sukansa da su ke yi.

To ku sani, kada rashin lafiyar Buhari ta tada muku hankali, kamar yadda Mallam Garba Shehu ya fada, Buhari ba cikin wani matsanancin yanayi ya ke ba, ko alama.

Ah, yo to ma idan kuna ganin abin da muke fada ba haka bane, ina hankulanku su ke? Ashe ba ku san rashin lafiyar ko wane shugaban qasa a duniyar nan babban labari ne ga manema labaran duniya ba? Shugaban Qasarku ne, amma a tunaninku kun fi kafafen yada labarai na qasa da qasa qishin ruwan son sanin halin da Buhari ya ke ciki da rawar qafar yadawa?

Balle Shugaban Qasa kamar Buhari, lamarinsa ya na maruqar daukan hankalin kafafen yada labaran qasa da qasa sabo da dalilai da yawa.

Ba na so in ja ku a wannan karon, amma insha Allah idan na sami zama zan dora daga inda na tsaya. Maganar dai ita ce kawai a ci gaba da yi wa Buhari addu'a, amma kowa ya kwantar da hankalinsa, insha Allah Buhari ya na tafe cikin nasara da Qarfin Mulkin Allah.

Tuesday 3 January 2017

Majnun Laila

LABARIN SOYAYYAR LAILA
MAJNUN
Waye majnun lailah? Wani mutumne da aka yi a daular banu umaiyya abisazance mafi inganci. Sunansa shine Qais Bn Mulawwah daga kabilar Banu Amir, Qais balaraben kauyene, ya taso tare da ‘yar gidan kawunsa mai suna LAILA
BNT MAHDI IBN SA’D Amfi sanin Laila da sunan Laila Aamiriya, tare suka taso tun suna yara suna kiwon dabobi har suka girma, suka fita daga sahun yara suka kai munzalin balagha.
A Yayin da alamun nuna balaga da cikar budurci suka gama bayyana ajikin Laila sai Qais ya rude soyayyarsa gare ta, hankalinsa ya dugunzuma ya tashi.
Domin a wannan lokacin ne Qais ya
Llura da irin kyawun dirin da Allah ya
yiwa abokiyarsa Laila, a kullum
soyayyar Laila sai kara tashin gwauron zabi take yi a cikin zuciyar Qais, a cikin wannan yanayi ne Qais ya shiga rera
mata waqoqin soyayya kala-kala babu dare babu rana hakance tasa Mahdi mahaifin Laila ya nemi da Qais ya fito dan maganar aure, saboda nuna soyayya da kauna said a Qais ya bayar da raquma hamsin gidansu Laila a matsayin kudin aure.
Ana haka sai ga wani mutum da ake
kira WIRD BN MUHAMMAD wani dan
hamshaqin attajiri ne daga cikin
‘ya’yayen masarautar Banu Umaiyya,
katsahan yayi ido hudu da Laila a wata rana a cikin wani Lambu tana kiwon dabobinta. Daga wannan rana Soyayyar Laila ta hana Wird ya yi bacci a wannan dare! Cikin yan kwanaki kadan Iyayen Wird suka sauka a gidan su Laila dan neman aurenta ga dansu
Wird. A wannan rana da Iyayan Wird
suka je ga mahaifin Laila said a suka
ajiye masa Manyan Raquma guda dari (100) a matsayin kudin aure, wato ribi biyu akan abinda Qais ya bayar! Daga nan lissafi ya kwacewa mahaifin Laila, domin kuwa yayi irin mugun abin kunyar nan na nuna kwadayi da son abin duniya. Bayan haka ne Mahaifin Laila ya kira ‘yarsa Laila cikin daki yanai mata hudunbar cewar ga mai kudi dan masu mulki shi zai aurawa ita! Babbar Magana! Laila taki amincewa da maganar mahaifinta a karon farko, amma sai ya yi mata barazanar cewar zai yanka ta idan har bata amince da auren Wird ba! Kwatsam sai aka wayi gari Qais ya ji gari ya dauka da kace nace din anyiwa masoyiyarsa Laila aure, da Wird. Wanne irin hali Qais zai kasance a wannan ranar? Tun daga wannan lokacin bacci yayi hijira daga idonsa, farin ciki ya gagari zuciyarsa, damuwa bakin ciki gami da bacin Rai da takaici, zubar da hawaye babu dare babu rana,
suka kasance tare da Qais a matsayin abokai na din-din-din!
Wake waken soyayya sune zancensa, bashi da abokin hira sai wakar da yake yiwa laila ga kadan daga irin abinda yake cewa:
zuwa ga Allah nake kai kukan son laila kamar yadda maraya yake kai kukan maraicinsa zuwa a Allah.
Marayanda da kafasa ta karye gashi
kuma dangi sun gujeshe
Lallai rasa iyaye abune mai girman
gaske.
Haka Qais da aka yiwa lakabi da
“Majnunu lailah” yake bin kwararo
kwararo da saman manyan duwatsu da bakin ruwa da cikin furanni yana
rerawa Laila wadannan baituka masu motsa zuciya bai gushe ba harse da akayi masa lakabi da “majnunu laila”....!
Duk da cewa itama Laila tana matukar son Qais(majnun) amma kuma hakan baya hanata ta wahalar dashi, a wasu lokutanma harda yi masa wulaqanci, baya ga yin amfani da mallakeshi da tayi wajen azabtar dashi, dama haka
sha’anin mata yake shi yasa majnun
awani baiti yace:
“Nace da wani babban malami da na
gamu dashi a makka, dan Allah ka bani
labarin wacce take cutar dani,
azamanin da take jiji da kai (saboda ina
sonta) shin hakan da take ba laifi
bane?” Sai Malamin ya fadawa Qais
cewa: “Wallahi da sannu azaba zata
shafe ta kuma a duniya ma saita hadu
da bala’I”. Dagan an Qai yace, sai na
kasa mallakar idona sai da hawaye ya
zubo cikin sauri ya jiqa min aljihun
rigata, sai nace, Allah ya yafe mata
laifinta duk da yake a duniya dan
kadanne samunta.
Qais ko Laila Majnun Bai gusheba a
cikin wannan hali har sai da ya samu
tabin hankali. Domin ya kasance idan
yaga yara suna wasan kasa yakan zauna
tare dasu ya taro kasa ya rinqa gina
gida irin wanda yara suke yi da kasa
yana cewa cikin waqa: “abokaina kuzo
kuga gidana nida laila”....!
A yayinda al-amari ya tsananta sai
mutane suka baiwa mahaifin Majnun
wato Qais shawara da ya daukeshi ya
kaishi ka’aba (dakin Allah) ya umarce
shi da ya roqi Allah ya cire masa son
Laila! Amma saboda tsananin soyayya a
yayin da suka je dakin ka’aba sai
mahaifinsa yace masa: kama tufafin
ka’aba ka roki Allah ya cire maka son
Laila sai Majnun ya kama yace: “Allah
na tuba gareka daga dukkan laifi,
amma bazan tuba daga son da nake
yiwa Laila ba . . . ataqaice haka majnun
ya rayu cikin wannan yanayi na abin
tausayi!
Ita kuwa Laila tuni wanda ya aureta ya
dauke daga kasar Saudiyya gabaki daya
zuwa kasar Iraqi. Haka itama ta rayu
cikin wannan mummunan yanayi
abinka da ‘ya mace mai rauni said a
rashin ganin Qais ya haddasa mata
ciwon zuciya .......! Daga nan ita ma ta
kamu da ciwon zuciya saboda tsananin
soyayyar Qais Majnun! Tana cikin
wannan hali ne na rashin ganin
masoyinta Allah ya karbi rayuwarta! A
lokacin da Majnun yaji labarin
rasuwarta sai da yaje har kasar Iraqi ya
nemi inda take, da inda aka binne ta, a
makabartar da aka binne laila a daidai
gindin kabarinta ya tare.....! Bashi da
aiki sai kuka da wakokin soyayya a
gareta. Wata rana da safe sai masu
wucewa suka hangoshi (Qais-Majnun) ya kifa cikinsa akan qabarinta, ko da aka zo aka duba sai aka tarar Allah ya yi masa cikawa! Haka fa Allah yakejarabtar wasu da soyayya, dan Hakka idan kaji Hasan na sambatu akan Hasana kada ka zargeshi.

Thursday 15 December 2016

HALIN DA SHI'A TA JEFA QASAR SYRIA

ALLAH KA CECI BAYIN KA NA SYRIA
DAGA  Malam Umar Mansur
Halab! Halab!! Halab!!!
HALAB KAFIN YAQI
Halab Tsohon garine me matuqar girma da muhimmanci ta fuskar tarihi da kasuwanci wanda shine gari na uku mafi girma bayan Istanbul (Qusdandaniyya) da Cairo a zamanin daular Usmaniyya ( othmon empire ).
Garin Halab shine gari mafi girma na biyu a Qasar Siriya wanda yake iyaka da qasar Turkiyya da nisan kilomita 48Km Sannan yana dauke da kimanin mutane miliyan hudu da suke rayuwa a cikinsa. Kamar yadda Jami'ar Halab na daya daga cikin manyan jami'oin qasar siriya me dauke da kimanin dalibai dubu goma sha shida masu karatu a fanni daban daban.
Hakanan Garin na Halab ya shahara da kamfanoni da masana'antun sarrafa auduga, siminti da sauransu wanda hakan yasa yazama daya daga cikin cibiyar hada hadar kasuwanci mafi girma a qasar.
HALAB A YAU !
Hakika duk
abinda zamu naqalto daga abinda mukaji ko muka gani ta kafafen sadarwa wani yanki ne na daga abinda yake faruwa a wannan gari na halab domin an wayi gari YAN SHI'A qarqashin jagorancin Basshar El-Asad da Qungiyoyin hadaka irinsu Iran, Hizbullah na Lebanon, Yan shi'a daga Pakistan, samarin shi'a daga ko ina na duniya tare da Sojojin Rasha karkashin jagorancin PUTIN suna gab da goge sunan halab daga Taswirar duniya(Map) .
An wayi gari saboda irin kisan kiyashi da kisan qare dangi da akeyi a wannan gari ana kimanta wanda suka rage a garin basu wuce mutane dubu dari uku da hamsin ba cikin miliyan hudu. Sannan Labari ya tabbata babu wani asibiti da ya rage a garin duk an rusasu ballantana magani balle ayi maganar likitoci kamar yadda ba a maganar abinci domin qungiyar qawancen yan shi'a qarqashin El-Asad duk sun rusasu sakamakon Harin da suke kaimusu ta sama da ta qasa.
An kama dayawa an kulle a gidan kaso , an azabtar dasu,an yanka na yankawa,an harbe na harbewa, an yi lalata da yara mata a gaban iyayansu sannan a kashesu, an kashe iyaye maza a gaban ya'yansu,anyi lalata da mata a gaban mijinta sannan a kasheta a gabansa ko a kashe miji a gaban matarsa, an kashe jarirai , yara qanana maza da mata, an rusa gidaje, makarantu, masallatai, kasuwanni, asibitoci da masana'antu.
A Yau ta kai a halab yara mata roqon iyayansu sukeyi su kashesu ko su duro daga saman bene su mutu dan kada ayi lalata dasu sannan a kashesu kisan wulakanci wanda akan hakan har fatawa suke nema.
A cikin Mako biyunnan da suka gabata an kashe sama da mutane dubu uku banda wanda suka ji ciwo da kuma wanda suka mace basu a raye basu a mace. Masu kisan nan fa duniya tasansu kuma tasan ko su waye kuma ta san dan me suke kisan amma dayake AHLUS SUNNAH ake kashewa kamar anyi ruwa an dauke babu maganar Human rights. Sannan duk wanda ya karanta Tarihi ze fahimci Jumhuriyar Iran ta yanzu Qoqari takeyi tayi abinda Kakansu SHAH -ISMAIL yayi bayan kafa daular Safawiyyun ta fuskar yada shi'anci takowace irin hanya shiyasa duk wani bala'i da wata fitina dake faruwa a duniyar musulunci a yanzu se kaga da sa hannun Iran a ciki kuma wallahi Tallahi lamarin nan kamar yadda malamina Dr Umar Mansur ya fadane a yau yan shi'a da zasu sami dama a ko ina toh zasuyi mafiyin abinda sukeyi yanzu haka a Halab. A don Haka Wallahi mudaina jin tausayin yan shi'a ko abinda aka musu a Najeriya domin in mukai sakaci ko wauta zamu zama nama a wajen mayunwaciyar kura ,Allah ya tsare.
Muna Roqon Allah ya kawoma yanuwanmu na Halab dauki na gaggawa kamar yadda muke roqansa da ya maida kaidin makirai akansu a duk inda suke.
Via Prince Farhanul Khair
Bursa/Turkey
15/12/2016