Thursday 15 December 2016

HALIN DA SHI'A TA JEFA QASAR SYRIA

ALLAH KA CECI BAYIN KA NA SYRIA
DAGA  Malam Umar Mansur
Halab! Halab!! Halab!!!
HALAB KAFIN YAQI
Halab Tsohon garine me matuqar girma da muhimmanci ta fuskar tarihi da kasuwanci wanda shine gari na uku mafi girma bayan Istanbul (Qusdandaniyya) da Cairo a zamanin daular Usmaniyya ( othmon empire ).
Garin Halab shine gari mafi girma na biyu a Qasar Siriya wanda yake iyaka da qasar Turkiyya da nisan kilomita 48Km Sannan yana dauke da kimanin mutane miliyan hudu da suke rayuwa a cikinsa. Kamar yadda Jami'ar Halab na daya daga cikin manyan jami'oin qasar siriya me dauke da kimanin dalibai dubu goma sha shida masu karatu a fanni daban daban.
Hakanan Garin na Halab ya shahara da kamfanoni da masana'antun sarrafa auduga, siminti da sauransu wanda hakan yasa yazama daya daga cikin cibiyar hada hadar kasuwanci mafi girma a qasar.
HALAB A YAU !
Hakika duk
abinda zamu naqalto daga abinda mukaji ko muka gani ta kafafen sadarwa wani yanki ne na daga abinda yake faruwa a wannan gari na halab domin an wayi gari YAN SHI'A qarqashin jagorancin Basshar El-Asad da Qungiyoyin hadaka irinsu Iran, Hizbullah na Lebanon, Yan shi'a daga Pakistan, samarin shi'a daga ko ina na duniya tare da Sojojin Rasha karkashin jagorancin PUTIN suna gab da goge sunan halab daga Taswirar duniya(Map) .
An wayi gari saboda irin kisan kiyashi da kisan qare dangi da akeyi a wannan gari ana kimanta wanda suka rage a garin basu wuce mutane dubu dari uku da hamsin ba cikin miliyan hudu. Sannan Labari ya tabbata babu wani asibiti da ya rage a garin duk an rusasu ballantana magani balle ayi maganar likitoci kamar yadda ba a maganar abinci domin qungiyar qawancen yan shi'a qarqashin El-Asad duk sun rusasu sakamakon Harin da suke kaimusu ta sama da ta qasa.
An kama dayawa an kulle a gidan kaso , an azabtar dasu,an yanka na yankawa,an harbe na harbewa, an yi lalata da yara mata a gaban iyayansu sannan a kashesu, an kashe iyaye maza a gaban ya'yansu,anyi lalata da mata a gaban mijinta sannan a kasheta a gabansa ko a kashe miji a gaban matarsa, an kashe jarirai , yara qanana maza da mata, an rusa gidaje, makarantu, masallatai, kasuwanni, asibitoci da masana'antu.
A Yau ta kai a halab yara mata roqon iyayansu sukeyi su kashesu ko su duro daga saman bene su mutu dan kada ayi lalata dasu sannan a kashesu kisan wulakanci wanda akan hakan har fatawa suke nema.
A cikin Mako biyunnan da suka gabata an kashe sama da mutane dubu uku banda wanda suka ji ciwo da kuma wanda suka mace basu a raye basu a mace. Masu kisan nan fa duniya tasansu kuma tasan ko su waye kuma ta san dan me suke kisan amma dayake AHLUS SUNNAH ake kashewa kamar anyi ruwa an dauke babu maganar Human rights. Sannan duk wanda ya karanta Tarihi ze fahimci Jumhuriyar Iran ta yanzu Qoqari takeyi tayi abinda Kakansu SHAH -ISMAIL yayi bayan kafa daular Safawiyyun ta fuskar yada shi'anci takowace irin hanya shiyasa duk wani bala'i da wata fitina dake faruwa a duniyar musulunci a yanzu se kaga da sa hannun Iran a ciki kuma wallahi Tallahi lamarin nan kamar yadda malamina Dr Umar Mansur ya fadane a yau yan shi'a da zasu sami dama a ko ina toh zasuyi mafiyin abinda sukeyi yanzu haka a Halab. A don Haka Wallahi mudaina jin tausayin yan shi'a ko abinda aka musu a Najeriya domin in mukai sakaci ko wauta zamu zama nama a wajen mayunwaciyar kura ,Allah ya tsare.
Muna Roqon Allah ya kawoma yanuwanmu na Halab dauki na gaggawa kamar yadda muke roqansa da ya maida kaidin makirai akansu a duk inda suke.
Via Prince Farhanul Khair
Bursa/Turkey
15/12/2016

No comments:

Post a Comment