Sunday 11 December 2016

NIGERIAN PEACE CORPS DA AL’UMMAR JIHAR KATSINA

NIGERIAN PEACE CORPS DA AL’UMMAR JIHAR
KATSINA
Kamar yadda mu ka ji kuma mu ka gani cewa
Mahukuntan Nigeria sun gabatar da qudurin su
na sanya wannan hukuma a cikin jerin
hukumomin tsaro na kasar Nigeria. Wannan yazo
a daidai lokacin da matasan kasar ke cikin halin
rashin aikin yi wadda samun damar kan ceci
matasa da yawa a wannan Kasa. Kusan ka iya
cewa jahohi da dama sun yi maraba da wannan
yunkurin na daukar ‘yan peace corps musamman
yadda ‘yan peace corps din suka dade suna ma
kungiyar hidima tsawon shekaru biyar, amman
ban da jiha ta Katsina inda wasu mutane ke ma
‘yan kungiyar kallon mayaudara, kusan kwana
biyar da su ka gabata dan uwa na Husain
Kyar'adua ya yi rubutu don ya bayyana ma
al’ummar jihar Katsina halin da ake ciki a jihar
dangane da kungiyar da kuma kokarin da
Kwamandan su yake na ganin ya ba Katsinawa
hakkinsu. A cikin rubutun nashi wasu masu ganin
cewa su sun waye da kafofin yada labarai na
zamani su kai ta maganganu wadanda za su sa
shakku musamman ga masu sha’awar shiga
kungiyar wanda ga alama basu san komi ba
game da batun.
HALIN DA KUNGIYAR TA KE CIKI A KATSINA
A wajan shekarar 2012 ne kungiyar ta bayyana a
jihar Katsina inda mafi akasarin wadanda su kai
rijista da kungiyar matakin karatun su bai wuce
na Sakandire ba, hakan ne ma yasa mutane
masu zurfin karatu su ka rena aikin suke masu
izgili kala-kala, ban mantawa akwai jajirtattu a
cikin ‘yan Peace corps din wadanda su kai ta
kokarin samar ma kungiyar gindin zama a
wannan jiha wanda karshe wasun su har
makarantun sakandire su kai balantiya suna
zuwa don rage ma malamai aiki, wannan kadan
ne daga jajircewarsu. To abun mamaki wanda
anan gaba zai iya kawo ma tsaffin ‘yan kungiyar
matsala shine rashin samun masu karatu mai
zurfi wadanda za su zama shuwagabanni a
matakin jiha da kasa wanda yanzun maganar da
ake adadin mutane 4000 ne aka ce an ba jihar
amman har yanzun basu samu mutane 500 ‘yan
asalin jihar wadanda su kai rijista ba,ranar
alhamis din da sukai rally akalla wadanda ba 'yan
jihar Katsina ba kusan mutum dari wadanda
galibin su graduate ne su ka zo sukai rijista a
quota Katsina. wannan na gwada cewa karshe
dole a cike gurbin su da ‘yan wasu jihohi
wadanda su ka dau abun da muhimmanci wanda
har an fara hakan.
Kan haka ne Hussain ya so ya jawo hankalin
al’umma cewa ayi himma wajan shiga aikin kada
ace wai sai Shugaban Kasa yasa hannu sannan
za a yi don a lokacin zai iya zama sai mai hanya,
ko kuma mu komo muna cizon yatsa muna zagin
wasu cewa sun kawo mutanen jihar su. Karamin
misali anan NPower ga kuma Civil Defense
wadanda aka rika ce masu kafi banga.
Kira naga al’umma shine mu yi kokari mu shiga
aikin nan don cike gurabun da aka tanadar ma
jihar. Sannan daga karshe ina kira ga duk mai iko
kan tallafa ma matasan jihar, to ga dama ta
samu ta taimakon rayuwar matasa.
An ruwaito cewa a Kano gwamnan su ya biya ma
mutum 2000 kudin shiga haka ma a jihar Yobe ya
biya ma mutum 3000. Mu kuma a jihar mu a na
tai masu yarfe.
ALLAH YA SA AL'UMMAR MU SU FARKA
Hasan Kabir Yaradua ( Hk Yaradua )
11/12/2016

No comments:

Post a Comment