Thursday 15 December 2016

HALIN DA SHI'A TA JEFA QASAR SYRIA

ALLAH KA CECI BAYIN KA NA SYRIA
DAGA  Malam Umar Mansur
Halab! Halab!! Halab!!!
HALAB KAFIN YAQI
Halab Tsohon garine me matuqar girma da muhimmanci ta fuskar tarihi da kasuwanci wanda shine gari na uku mafi girma bayan Istanbul (Qusdandaniyya) da Cairo a zamanin daular Usmaniyya ( othmon empire ).
Garin Halab shine gari mafi girma na biyu a Qasar Siriya wanda yake iyaka da qasar Turkiyya da nisan kilomita 48Km Sannan yana dauke da kimanin mutane miliyan hudu da suke rayuwa a cikinsa. Kamar yadda Jami'ar Halab na daya daga cikin manyan jami'oin qasar siriya me dauke da kimanin dalibai dubu goma sha shida masu karatu a fanni daban daban.
Hakanan Garin na Halab ya shahara da kamfanoni da masana'antun sarrafa auduga, siminti da sauransu wanda hakan yasa yazama daya daga cikin cibiyar hada hadar kasuwanci mafi girma a qasar.
HALAB A YAU !
Hakika duk
abinda zamu naqalto daga abinda mukaji ko muka gani ta kafafen sadarwa wani yanki ne na daga abinda yake faruwa a wannan gari na halab domin an wayi gari YAN SHI'A qarqashin jagorancin Basshar El-Asad da Qungiyoyin hadaka irinsu Iran, Hizbullah na Lebanon, Yan shi'a daga Pakistan, samarin shi'a daga ko ina na duniya tare da Sojojin Rasha karkashin jagorancin PUTIN suna gab da goge sunan halab daga Taswirar duniya(Map) .
An wayi gari saboda irin kisan kiyashi da kisan qare dangi da akeyi a wannan gari ana kimanta wanda suka rage a garin basu wuce mutane dubu dari uku da hamsin ba cikin miliyan hudu. Sannan Labari ya tabbata babu wani asibiti da ya rage a garin duk an rusasu ballantana magani balle ayi maganar likitoci kamar yadda ba a maganar abinci domin qungiyar qawancen yan shi'a qarqashin El-Asad duk sun rusasu sakamakon Harin da suke kaimusu ta sama da ta qasa.
An kama dayawa an kulle a gidan kaso , an azabtar dasu,an yanka na yankawa,an harbe na harbewa, an yi lalata da yara mata a gaban iyayansu sannan a kashesu, an kashe iyaye maza a gaban ya'yansu,anyi lalata da mata a gaban mijinta sannan a kasheta a gabansa ko a kashe miji a gaban matarsa, an kashe jarirai , yara qanana maza da mata, an rusa gidaje, makarantu, masallatai, kasuwanni, asibitoci da masana'antu.
A Yau ta kai a halab yara mata roqon iyayansu sukeyi su kashesu ko su duro daga saman bene su mutu dan kada ayi lalata dasu sannan a kashesu kisan wulakanci wanda akan hakan har fatawa suke nema.
A cikin Mako biyunnan da suka gabata an kashe sama da mutane dubu uku banda wanda suka ji ciwo da kuma wanda suka mace basu a raye basu a mace. Masu kisan nan fa duniya tasansu kuma tasan ko su waye kuma ta san dan me suke kisan amma dayake AHLUS SUNNAH ake kashewa kamar anyi ruwa an dauke babu maganar Human rights. Sannan duk wanda ya karanta Tarihi ze fahimci Jumhuriyar Iran ta yanzu Qoqari takeyi tayi abinda Kakansu SHAH -ISMAIL yayi bayan kafa daular Safawiyyun ta fuskar yada shi'anci takowace irin hanya shiyasa duk wani bala'i da wata fitina dake faruwa a duniyar musulunci a yanzu se kaga da sa hannun Iran a ciki kuma wallahi Tallahi lamarin nan kamar yadda malamina Dr Umar Mansur ya fadane a yau yan shi'a da zasu sami dama a ko ina toh zasuyi mafiyin abinda sukeyi yanzu haka a Halab. A don Haka Wallahi mudaina jin tausayin yan shi'a ko abinda aka musu a Najeriya domin in mukai sakaci ko wauta zamu zama nama a wajen mayunwaciyar kura ,Allah ya tsare.
Muna Roqon Allah ya kawoma yanuwanmu na Halab dauki na gaggawa kamar yadda muke roqansa da ya maida kaidin makirai akansu a duk inda suke.
Via Prince Farhanul Khair
Bursa/Turkey
15/12/2016

Sunday 11 December 2016

NIGERIAN PEACE CORPS DA AL’UMMAR JIHAR KATSINA

NIGERIAN PEACE CORPS DA AL’UMMAR JIHAR
KATSINA
Kamar yadda mu ka ji kuma mu ka gani cewa
Mahukuntan Nigeria sun gabatar da qudurin su
na sanya wannan hukuma a cikin jerin
hukumomin tsaro na kasar Nigeria. Wannan yazo
a daidai lokacin da matasan kasar ke cikin halin
rashin aikin yi wadda samun damar kan ceci
matasa da yawa a wannan Kasa. Kusan ka iya
cewa jahohi da dama sun yi maraba da wannan
yunkurin na daukar ‘yan peace corps musamman
yadda ‘yan peace corps din suka dade suna ma
kungiyar hidima tsawon shekaru biyar, amman
ban da jiha ta Katsina inda wasu mutane ke ma
‘yan kungiyar kallon mayaudara, kusan kwana
biyar da su ka gabata dan uwa na Husain
Kyar'adua ya yi rubutu don ya bayyana ma
al’ummar jihar Katsina halin da ake ciki a jihar
dangane da kungiyar da kuma kokarin da
Kwamandan su yake na ganin ya ba Katsinawa
hakkinsu. A cikin rubutun nashi wasu masu ganin
cewa su sun waye da kafofin yada labarai na
zamani su kai ta maganganu wadanda za su sa
shakku musamman ga masu sha’awar shiga
kungiyar wanda ga alama basu san komi ba
game da batun.
HALIN DA KUNGIYAR TA KE CIKI A KATSINA
A wajan shekarar 2012 ne kungiyar ta bayyana a
jihar Katsina inda mafi akasarin wadanda su kai
rijista da kungiyar matakin karatun su bai wuce
na Sakandire ba, hakan ne ma yasa mutane
masu zurfin karatu su ka rena aikin suke masu
izgili kala-kala, ban mantawa akwai jajirtattu a
cikin ‘yan Peace corps din wadanda su kai ta
kokarin samar ma kungiyar gindin zama a
wannan jiha wanda karshe wasun su har
makarantun sakandire su kai balantiya suna
zuwa don rage ma malamai aiki, wannan kadan
ne daga jajircewarsu. To abun mamaki wanda
anan gaba zai iya kawo ma tsaffin ‘yan kungiyar
matsala shine rashin samun masu karatu mai
zurfi wadanda za su zama shuwagabanni a
matakin jiha da kasa wanda yanzun maganar da
ake adadin mutane 4000 ne aka ce an ba jihar
amman har yanzun basu samu mutane 500 ‘yan
asalin jihar wadanda su kai rijista ba,ranar
alhamis din da sukai rally akalla wadanda ba 'yan
jihar Katsina ba kusan mutum dari wadanda
galibin su graduate ne su ka zo sukai rijista a
quota Katsina. wannan na gwada cewa karshe
dole a cike gurbin su da ‘yan wasu jihohi
wadanda su ka dau abun da muhimmanci wanda
har an fara hakan.
Kan haka ne Hussain ya so ya jawo hankalin
al’umma cewa ayi himma wajan shiga aikin kada
ace wai sai Shugaban Kasa yasa hannu sannan
za a yi don a lokacin zai iya zama sai mai hanya,
ko kuma mu komo muna cizon yatsa muna zagin
wasu cewa sun kawo mutanen jihar su. Karamin
misali anan NPower ga kuma Civil Defense
wadanda aka rika ce masu kafi banga.
Kira naga al’umma shine mu yi kokari mu shiga
aikin nan don cike gurabun da aka tanadar ma
jihar. Sannan daga karshe ina kira ga duk mai iko
kan tallafa ma matasan jihar, to ga dama ta
samu ta taimakon rayuwar matasa.
An ruwaito cewa a Kano gwamnan su ya biya ma
mutum 2000 kudin shiga haka ma a jihar Yobe ya
biya ma mutum 3000. Mu kuma a jihar mu a na
tai masu yarfe.
ALLAH YA SA AL'UMMAR MU SU FARKA
Hasan Kabir Yaradua ( Hk Yaradua )
11/12/2016

Sunday 20 November 2016

Gangamin Tallafin Yan Gudun Hijira

#GANGAMINTALLAFINIDPS: GARABASA TA SAMU - HANYAR RAHMA KAI TSAYE! 
الراحمون يرحمهم الرحمان ارحموا من فى الأرض يرحمكم من فى السماء
Masu tausayi, Allah Mai Rahma Ya na tausaya ma su. Ku tausayawa bayin Allah a bayan Kasa, sai Allah Mai Rahma da ke Sama Ya yi maku Rahma!
1. SHIN KUN SAN HALIN DA YAN GUDUN HIJIRA KE CIKI A BORNO A YANZU?
Daure ku biyo mu domin ziyarar gani da ido a wurare daban-dabam na 'yan Gudun hijira a Jihar Borno.

2. Ko kun San cewa Al'ummar Musulmin Jihar Kano sun aika Tallafin gaggawa na Trailer 10 ta abinci da Tufafi da qimarsu ta fi #200,000,000 (Naira Miliyan Dari Biyu) kuma mun je mun raba hannu da hannu ga wadanda suka cancanta? 

3. Ko Allah Ya sa kuna cikin wadanda suka tallafa da Abinci ko Tufafi ko kudi don wannan aikin?
Ku biyo mu a shafinmu na facebook don ganin hotuna da videos na Al'ummar da muka kai wa tallafin da yanda muka damka amanar da kuka dora mana.

4. Ko ka yi shirin fara bada tallafinka na akalla N1,000 a wata don ceto wadannan bayin Allah daga yunwa da CUTUTTUKA?
Ka na iya turowa kai tsaye ta wadannan lambobin account:
JAIZ BANK 000 0024 550 ko StanbicIBTC 000 123 6900
Sunan Account: Council of Ulama Kano

5. Shin kun shirya bada gudunmawar ku ta wasu hanyoyi daban dabam?
Ku tuntu6e mu kai tsaye:
    A. Dr Said Ahmad Dukawa (0701 211 9622) or
   B. Engr  Basheer Adamu Aliyu (0815 738 3838)

6. Shaitan ya hana ka yin wadancan duka? 
Kar ka bari ya hana ka aikawa da wannan sakon ta hanyar facebook ko whatsapp da sauran su.
Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya ce "duk wanda ya yi nuni ga alheri zai samu lada kamar wanda ya aikata alherin."

Sunday 30 October 2016

Abubuwan Da Yariman Saudiya Yayi Kafin Rataye shi

Abubuwan Da Yariman Saudiya  Yayi Kafin  Rataye Shi-- Darasi Ga Kowa

Ismai'l Karatu Abdullahi

Kasar Saudiya, kasacewarta ta yi ƙaurin suna a duniya kan gudanar da hukuncinta kan gaskiya ga duk wanda ya aikata abunda bai dace ba, tana hukunci ne daidai da abunda ya aikata. Kutunan Saudiya masu adalci ne, basu bambamtawa wajen zartar da hukunci.

Wani abun misali ya faru a ranar 18 ga watan Oktoban shekara ta 2016,  inda aka rataye wani basarake ta dalilin kashe wani ɗan Saudiya mazauni ƙasar.

Yariman mai suna Turki Bin Saud Bin Turki Bin Saud Al Kabeer, an rataye shi. An yi masa haka ne daidai da abunda ya aikata kamar yadda dokan ƙasarsu ya kasance.

Yariman, mintuna kaɗan kafin a rataye shi, yayi wasu abubuwa  waɗanda za su kasance darasi a gare mu.

Ga kamar yadda ya yi: An Kashe Saud Bin Turki ne bisa kisan gilla da yayi wa wani- Adalci ga Kowa.

Mintuna kaɗan kafin rataye shi, ya nemi a bar shi ya gana da iyalanshi, kuma ya samu. Ya ɗauki kimanin awanni 4 tare da iyayensa da danginsa,  ba sai an yi bayanin abunda ya gudana ba kowa zai iya sani kamar yin ban kwana, ƙarfafa masa zunciya da neman gafara.

Daga bisani sai Limamin Masallacin Al Safa ya ce a ɗauko shi daga ganawar da iyalinsa waɗanda suka ta kiran sunanshi suna bankwana , babu abunda za ta ji sai kuka da alamun baƙin ciki. 

Muhammad Al Maslookhi ne ya watsa a shafinsa na "Twitter", Su kuma Shafin Saudi "News site Al Marsad", suka ruwaito.

Masu rataya suka ɗauke shi zuwa ofishin 'yan sanda inda nan ne zai rubuta wasiyarsa ta ƙarshe, amma bai iya rubutawa ba.

Da misalin karfe 11 na safe, iyalan wanda  Yariman ya kashe, suka iso inda aka sanar da su za a rataye ahi.

Yariman, yayi alwala, sannan ya jira lokacin da za a rataye shi.

Babba wansa, yayi ƙoƙarin magana da iyalin wanda  Yariman ya kashe   domin nema wa ƙaninsa gafara, da kuma ko zasu karɓi diyya, a yinkuri na karshe kafin a rataye Yariman amma sun ƙi yarda.

Bayan sallar Azahar, 'yan'uwan Yariman suka sake neman wannan alfarman daga iyayen waɗanda aka kashe amma sun ƙi amincewa.
    
Kamar yadda kuka sani musulunci ba addini ba ne mai danne hakkin kowa ba. Kamar yadda 'yan'uwan Yarima suka nemi iyalan wanda Yarima ya kashe da su karɓi diyya amma suka ƙi, don haka dole a zartar wa Yariman hukunci daidai da abunda ya aikata.

Yarima yayi sallar Azahar da La'asar. Bayan nan da karfe 4:13  aka rataye shi. Har aka rataye shi, babu abinda ya ke fitowa daga bakinshi sai karatun Alkur'ani da ambaton neman yafiya ga Allah.

Kar ku manta, an rataye Yariman ne sakamakon kashe wani da yayi da bindiga.

Addu'armu Allah Ya gafarta wa wanda aka kashe da shi da yayi kashin.

©Zuma Times Hausa

SHUGABA BUHARI YA YI ALLAH WA'AZI DA HARIN YAN SHI'A A DAKIN ALLAH

Shugaba Buhari ya yi Allah-wadai da harin 'yan shi'a a kan Dakin Allah.

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da harin da aka kai da makami mai linzami kan garin Makkah. Kanfanin Dillacin Labarai na Qasa mai Tsarki, Saudi Press Agency (SPA) ya ruwaito cewa Shugaba Buhari ya kira Sarki Salmanu dan AbdulAziz Alu Sa'ud, inda bayan ya jajanta masa mugun nufin da aka nufi garin na Makkah, ya yi addu'ar Allah Ya ci gaba da tsare garin Makkah da TsarewarSa da dukan Musulmi.

Shi ma Sarki Salman ya roqi Allah Ya taimaki Nigeria Ya kaita ga cin nasara, Ya kuma kareta daga sharrin maqiya.

http://spa.gov.sa/1553765

Haqiqa wannan waya ta Buhari ta qara nuna irin qaunar da Baban ya ke da ita ga Dakin Allah da ma Qasa mai Tsarki.

Allah Ya taimaki Baba Buhari Ya tsare shi da TsarewarSa. Allah Ya tozarta duk masu yunqirin cutar da DakinSa Ya hana musu biyan buqata.

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=1599634673396214&id=100000490902329&ref=bookmarks

Saturday 29 October 2016

Friday 28 October 2016

WA'AZIN WALIMAR AURE

WA'AZI DA WALIMAR AURE NA GIDAN SHEIK HABIBU YAHYA KAURA
DAGA CIKIN MALAMAI
1. Sheik Abdullahi Bala Lau
2. Sheik Kabir Gombe
idan Allah ya kai mu gobe Katsinawa za su sha WA'AZI daga Manyan Malamai na Jibwis ta kasa
Wa'azin zai gudana gobe ASABAR 29/10/16 a Masalacin Kerau,  Bayan Sallar Isha'i.
Mai masaukin Baki Sheik Yakubu Musa Katsina