Sunday 30 October 2016

Abubuwan Da Yariman Saudiya Yayi Kafin Rataye shi

Abubuwan Da Yariman Saudiya  Yayi Kafin  Rataye Shi-- Darasi Ga Kowa

Ismai'l Karatu Abdullahi

Kasar Saudiya, kasacewarta ta yi ƙaurin suna a duniya kan gudanar da hukuncinta kan gaskiya ga duk wanda ya aikata abunda bai dace ba, tana hukunci ne daidai da abunda ya aikata. Kutunan Saudiya masu adalci ne, basu bambamtawa wajen zartar da hukunci.

Wani abun misali ya faru a ranar 18 ga watan Oktoban shekara ta 2016,  inda aka rataye wani basarake ta dalilin kashe wani ɗan Saudiya mazauni ƙasar.

Yariman mai suna Turki Bin Saud Bin Turki Bin Saud Al Kabeer, an rataye shi. An yi masa haka ne daidai da abunda ya aikata kamar yadda dokan ƙasarsu ya kasance.

Yariman, mintuna kaɗan kafin a rataye shi, yayi wasu abubuwa  waɗanda za su kasance darasi a gare mu.

Ga kamar yadda ya yi: An Kashe Saud Bin Turki ne bisa kisan gilla da yayi wa wani- Adalci ga Kowa.

Mintuna kaɗan kafin rataye shi, ya nemi a bar shi ya gana da iyalanshi, kuma ya samu. Ya ɗauki kimanin awanni 4 tare da iyayensa da danginsa,  ba sai an yi bayanin abunda ya gudana ba kowa zai iya sani kamar yin ban kwana, ƙarfafa masa zunciya da neman gafara.

Daga bisani sai Limamin Masallacin Al Safa ya ce a ɗauko shi daga ganawar da iyalinsa waɗanda suka ta kiran sunanshi suna bankwana , babu abunda za ta ji sai kuka da alamun baƙin ciki. 

Muhammad Al Maslookhi ne ya watsa a shafinsa na "Twitter", Su kuma Shafin Saudi "News site Al Marsad", suka ruwaito.

Masu rataya suka ɗauke shi zuwa ofishin 'yan sanda inda nan ne zai rubuta wasiyarsa ta ƙarshe, amma bai iya rubutawa ba.

Da misalin karfe 11 na safe, iyalan wanda  Yariman ya kashe, suka iso inda aka sanar da su za a rataye ahi.

Yariman, yayi alwala, sannan ya jira lokacin da za a rataye shi.

Babba wansa, yayi ƙoƙarin magana da iyalin wanda  Yariman ya kashe   domin nema wa ƙaninsa gafara, da kuma ko zasu karɓi diyya, a yinkuri na karshe kafin a rataye Yariman amma sun ƙi yarda.

Bayan sallar Azahar, 'yan'uwan Yariman suka sake neman wannan alfarman daga iyayen waɗanda aka kashe amma sun ƙi amincewa.
    
Kamar yadda kuka sani musulunci ba addini ba ne mai danne hakkin kowa ba. Kamar yadda 'yan'uwan Yarima suka nemi iyalan wanda Yarima ya kashe da su karɓi diyya amma suka ƙi, don haka dole a zartar wa Yariman hukunci daidai da abunda ya aikata.

Yarima yayi sallar Azahar da La'asar. Bayan nan da karfe 4:13  aka rataye shi. Har aka rataye shi, babu abinda ya ke fitowa daga bakinshi sai karatun Alkur'ani da ambaton neman yafiya ga Allah.

Kar ku manta, an rataye Yariman ne sakamakon kashe wani da yayi da bindiga.

Addu'armu Allah Ya gafarta wa wanda aka kashe da shi da yayi kashin.

©Zuma Times Hausa

SHUGABA BUHARI YA YI ALLAH WA'AZI DA HARIN YAN SHI'A A DAKIN ALLAH

Shugaba Buhari ya yi Allah-wadai da harin 'yan shi'a a kan Dakin Allah.

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da harin da aka kai da makami mai linzami kan garin Makkah. Kanfanin Dillacin Labarai na Qasa mai Tsarki, Saudi Press Agency (SPA) ya ruwaito cewa Shugaba Buhari ya kira Sarki Salmanu dan AbdulAziz Alu Sa'ud, inda bayan ya jajanta masa mugun nufin da aka nufi garin na Makkah, ya yi addu'ar Allah Ya ci gaba da tsare garin Makkah da TsarewarSa da dukan Musulmi.

Shi ma Sarki Salman ya roqi Allah Ya taimaki Nigeria Ya kaita ga cin nasara, Ya kuma kareta daga sharrin maqiya.

http://spa.gov.sa/1553765

Haqiqa wannan waya ta Buhari ta qara nuna irin qaunar da Baban ya ke da ita ga Dakin Allah da ma Qasa mai Tsarki.

Allah Ya taimaki Baba Buhari Ya tsare shi da TsarewarSa. Allah Ya tozarta duk masu yunqirin cutar da DakinSa Ya hana musu biyan buqata.

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=1599634673396214&id=100000490902329&ref=bookmarks

Saturday 29 October 2016

ZAGIN SAHABBAI A WAJAN YAN SHI'A


ALLAH KA LA'ACI WADANAN ZINDIQAN YAN SHI'AR MASU ZAGIN SAHABBAI


Friday 28 October 2016

WA'AZIN WALIMAR AURE

WA'AZI DA WALIMAR AURE NA GIDAN SHEIK HABIBU YAHYA KAURA
DAGA CIKIN MALAMAI
1. Sheik Abdullahi Bala Lau
2. Sheik Kabir Gombe
idan Allah ya kai mu gobe Katsinawa za su sha WA'AZI daga Manyan Malamai na Jibwis ta kasa
Wa'azin zai gudana gobe ASABAR 29/10/16 a Masalacin Kerau,  Bayan Sallar Isha'i.
Mai masaukin Baki Sheik Yakubu Musa Katsina

Thursday 27 October 2016

DON MATASA

​​SHIRIN DON MATASA​

​DA'AWAH ​​​FAMILY SUPPORT ASSOCIATION​​​​

Na farin cikin gayyatar matasa Maza/Mata zuwa shiri na musamman da ta shirya kamar haka
A dakin taro na Social Dev, Filin Samji Katsinah,  A gobe Juma'a 28/10/16 da misalin karfe 3:00 pm

*​​​​YA KU MATASA KAR KU BARI A BAKU LABARI​​​*

​​​​​​MUNA MAKU MARABA​​​​​​

Wednesday 26 October 2016

Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahadar Husaini (R.A) (3)

Dr. . Muhd Sani Rijiyar Lemo
Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahadar Husaini (R.A) (3)

Assalamu Alaikum,
A baya mun ji yadda Marubucinmu da abokan
tafiyarsa suka auka cikin wani kango wanda
waɗansu gungun mutane suke zaune cikinsa, ana
rera musu waƙe suna amshi. To mai ya faru
bayan shigarsu. As-Sheikh Ali at-Tantawi ya ci
gaba da cewa,
“Muka tsallaka sahu-sahu muka shiga. Jama’a na
zazzaune, duk sun yi shiru, kamar mutuwa ta
gitta, bayan da shi mawaƙin ya yi shiru, da alama
dai hutawa suke yi kafin su ci gaba.
Mun kutsa ciki ne har sai da muka isa sahun
farko inda mai bayar da waƙe yake bayarwa.
Yana zaune a kan kujera, a gefe da shi akwai
wasu ƙarin kujeru waɗanda babu kowa a kansu,
sai aka ba mu muka zauna. Ba da jimawa ba aka
ci gaba da rera waƙe. Duk sa’adda mawaƙin ya
rera wasu baitoci sai ya ɗan dakata kaɗan, can
sai ka ga su kuma sauran jama’ar sun ɗaga
hannuwansu sama sun tattake sun bugi ƙirajesu
da su, ji kake wani jib!! kamar katangar wannan
kango tana motsawa saboda ƙarar wannan bugun
ƙirji da suka yi. Sannan ya sake rera wasu
baitocin, su kuma su sake jibga hannuwansu a
kan ƙirajensu, har sai da ƙirajensu suka yi ja jawur
saboda tsananin duka, gumi ya jiƙa su sharkaf.
Kowa a cikinsu yana cike da baƙin-ciki da jimami
na abin da aka yi wa Husaini (R.A), zuciyarsa
kuma ta cika da gaba da ƙiyayya ga Banu
Umayya da mutanen Sham, waɗanda wannan
waƙen ya ɗorawa alhakin jinin Husaini (R.A).
Ana tsakar haka ne, sai kawai ɗaya daga cikin
ɗaliban da muke tare da su, allurar kirkinsa ta
motsa, sai ya mike tsaye wai zai gabatar da ni a
wajen wannan mawaƙi don ya nuna masa irin
ƙaunarsa gare ni, tare da fada masa girman
matsayina da martaba ta a gurinsu. Sai jin shi na
yi yana faɗawa maƙin nan cewa, ‘Wannan babban
malaminmu ne, kuma mutumin ƙasar Sham ne,
sannan kuma babban marubuci ne, ya yi wallafe-
wallafe dadama, a cikin littattafansa da akwai
littafinsa ma mai suna ‘Abubakar As-Siddiq’, da
kuma wani mai suna ‘Umar bn Alkhattab’, da …
da…” ya ci gaba da lissafa su. Ina!! Ai ban gama
jin ƙarshen maganarsa ba, sai kawai na shiga yin
kalmar shahada, don ta zama mini ita ce ƙarshen
maganata a zamana na duniya.
Ban sake fahimtar abin da wannan ɗalibi nawa
yake faɗa wa wannan mawaƙi ba, domin zuciyata
tini ta ɓallo ta faɗo ƙasan cikina, kamar yadda
kasan irin yadda ‘lifter’ take faɗowa daga dogon
bene yayin da sarƙoƙin dake ɗauke da ita suka
tsinke. Kawai ni a lokcin na saddaƙar mutuwa zan
yi. Na juya ina ta dube-dube ko zan ga maguda,
amma ina! Wuri ya cika maƙil, ga katanga ta
kewaye ko ina, babu mafita sai wannan ƙofar
ɗaya da muka shigo daga gare ta, tsakanina ko
da ita ban da waɗannan mutane masu kirji a
waje ba abin da nake gani. Sannan me kake
zaton zai faru idan mutanen nan suka gane
cewa, ni mutumin Sham ne?! Kuma ni ne
mawallafin littfin tarihin Abubakar da Umar?! Ta
yaya zan yi in tabbatar musu cewa, babu
hannuna a cikin kashe Husaini?! Kuma babu
hannun kakanni na a ciki, saboda su ‘yan asalin
ƙasar Masar ne, ba mutanen Sham ba ne?! Don
haka su fahimci babu hannuwansu a kashe
Husaini. Wai ma tukunna ma za su ba ni damar
in kare kaina ne har da zan musu wannan
bayanin? Kuma ma idan na yi ƙokarin kare kaina,
kuna ga ma za su yarda da ni ne har su gaskata
ni?!
Daga nan kawai na sakankance na gama yawo,
yau sai buzuna, abin da ya rage mini shi ne in ci
gaba da yin addu’a a asirce, idan na zo mutuwa
in yi mutuwa mai sauƙi, amma babu maganar
kubuta.
Shi kuma abokina Anwar fa, mai yake ciki, domin
shi ne ya shigar da mu wannan matsalar. Da na
saci kallosa sai na ga kamanninsa sun canza,
launinsa ya canza kala, ya koma ruwan kalar
lemon tsami. Na kalli fuskar Sayyid mai koren
rawani ko zan fahimci matakin da yake shirin
ɗauka a kain, sai ban fahimci komai daga
wajensa ba, na dai bar al’amarina a wajen Allah.
Muka ɗauki tsawon awanni saba’in a jere cikin
wannan hali na fargaba da firgici da tsoro, babu
wani abu da ya canza. Duk wani minti ɗaya
matsayin awa ɗaya nake ganinsa. Aka ci gaba da
waƙe har aka kai ƙarshe. Can sai na kula mutane
su fara shirin fita, don na ga suna ta ɗauko
rigunansu suna mayarwa jikinsu. To daga nan ne
na fahimci matsalata dai ta zo ƙarshe, hankalina
ya fara dawo wa jikina. Na dubi agogona sai na
ga ashe ba awanni saba’in muka yi ba, mintina
ashirin ne kachal. Tsabar dai tsananin firgicewa
ne kawai ya sanya na ga tsawon lokacin. Daga
nan na yi bankwana da ‘Sayyid’ na nufi ƙofa na
fita. Na ji ni kamar na mutu na dawo Duniya.
Muka kwana biyu a Hillah. Da muka sake haɗuwa
da ‘Sayyid’ muka tattauna, sai na fahimci shi ba
mai tsattsauran ra’ayi ne ba, (ko kuma dai taƙiyya
ya yi min). Sai nake tuna masa abin da ya faru,
sai ya ce, “Ka godewa Allah da ya kuɓutar da
kai, kuma bai bar wannan jama’a sun ji abin da
wannan ɗalibi naka ya fada ba”. Sai na ce, “Ashe
kai ba za ka kare ni ba idan sun so auka min?
Sai ya yi dariya ya ce, “Idan na kare ka, ni kuma
wanene zai kare ni?! Wallahi ba wata kariya da
zan ba ka, zan ƙale ka da su, ka fuskanci
makomarka!’…”.
Wannan shi ne yadda babban marubucinmu
Sheikh Ali At-Tantawi ya tsallake rijiya da baya,
yayin da ya tsinci kansa a tsakiyar ƙatti madaka-
ƙiraza, a Husainiyya ta garin Hilla cikin Ƙasar Iraƙi.
Ya rubuta wannan labari na shi a cikin littafinsa
mai suna ‘Az-Zikrayāt’, juzu’i na 3, shafi na
379-388. Allah ka ganar da su gaskiya. Amin

Tuesday 25 October 2016

Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahad Husaini (R.A) (2)

  

 Na Ga ‘Mutuwa’ A Ranar Tunawa Da Shahada                            Husaini (R.A) (2)


Dr.Muhd Sani R/Lemu


‘Yan uwana masu karatu, kamar yadda na yi
muku alkawari a baya cewa, zan tsakuro muku
wani abu mai kama da taɓa-ka-lashe daga
cikin rubutun babban marubucin nan Ash-
Sheikh Ali at-Tantawi da ya rubuta ƙarkashin
waccen matashiya ta sama, a littafinsa mai
suna “Az-Zikrayaat” wato ‘Tuna Baya’. Ka da
ku manta na faɗa muku cewa, ba zan iya kawo
rubutunsa yadda yake ba, cike da fasaharsa da
taswirarsa, sai dai in kwatanta, domin an ce,
‘linzami ya fi ƙarfin bakin kaza’.
Malam dai ɗan asalin ƙasar Syria ne, amma ya
yi zaman karatu a Masar, sannan ya koyar a
Iraƙi, ya ziyarci wasu ƙasashe dadama, daga
ƙarshe ya yada zango a ƙasar Saudiya, a nan
Allah ya yi masa rasuwa a shekarar (1999
A.D). A zamansa a Bagadaza ta ƙasar Iraƙi ya
fita wata rana inda ya ga ‘mutuwa’ amma Allah
ya kuɓutar da shi, daga baya ya yi rubutu a
kan wannan labari, inda yake cewa,
“Ranar Ashura a Iraƙi wata rana ce ta daban.
Duk garin yakan koma tamkar ana zaman
makoki, kai ka ce, jiya-jiyan nan ne aka kashe
Husaini (r), ko kuma ka ce har yanzu Banu
Umayya ne ke rike da ragamar mulki; ko kuma
wadanda aka kashe Sayyidina Husaini (r) tare
da su, su ne a kan kujerar mulki. Mutane sun
manta da cewa, Duniyar fa ta canza, wasu
ƙasashe sun gushe, wasu kuma sun kafu,
komai a doron ƙasa ya canza akan yadda da
yake, kaɗai al’adar waɗannan mutane ne ita ce
ba ta canza ba har yanzu, jiya-a-yau.
Mu Musulmi duka muna son Annabi (S.A.W),
duk wanda ma ba ya son shi fiye da yadda
yake son kansa to imaninsa bai cika ba. Kuma
muna son duk mai son Manzon Allah (S.A.W).
Kuma jikokinsa Hasan da Husaini suna son shi,
don haka mu ma muna sonsu, muna son iyalan
gidan Manzon Allah duka, don haka ne ma
muke sa su a cikin salatin da muke yi wa
Annabi (S.A.W). Amma duk da haka ba za mu
taɓa yarda mu aikata abin da Annabi bai yi
umarni da aikata shi ba, don kuwa ba za mu
saɓa masa ba mu riƙa yin gaban-kanmu. Abin
da muka ga wasu mutane a Iraƙi suna yi ya
saɓawa koyarwar Annabi (S.A.W) kuma ba zai
taɓa amincewa da haka ba.
A wannan rana ta Ashura Abokina Anwar ya
buƙaci mu tafi garin Hillah (yanki ne na ‘yan
shi’a a Iraƙi) yawon buɗe ido. Sai na yarda.
Kuma muka nemi wasu ɗalibanmu su uku su yi
mana rakiya. A cikinsu akwai wani basamuden
ɗalibi, idan na tsaya kusa da shi dakyar kaina
yakan gota kwankwasonsa kaɗan, wani lokaci
ma nakan tsokane shi in ce masa, wai kai ba
ka gamuwa da matsalar iskar shaƙa (Oxygen) a
sararin samaniya idan kana tsaye?!. Amma
kuma duk da haka yaro ne mai kirki, mai
kyawawan halaye, sunanshi Abdullahi Adi. Ka ji
sunan shi ma ‘Adi’ kamar sauron ɓurɓushin
Adawa mutanen Annabi Hudu. (A.S). Sauran
ɗaliban guda biyu, ɗayansu ɗan Sunna ne,
gudan kuma ɗan Shi’a ne.
Kashe Sayyidana Husaini wata mummunar
aika-aika ce, e, zan sake maimaitawa,
mummunar aika-aika ce, a fahimci hakan da
kyau. To fa amma da jimawa wasu mawaƙa da
marubuta Adabin larabawa sun yi ta ƙarin
gishiri mai yawa a wajen bayanin wannan
‘aika-aika’ domin sun mayar da ita wani fage
na sukuwar dawakan adabinsu, da sakin
linzamin waƙoƙinsu. Lalle kam sun yi sukuwa
yadda suke so, to amma fa sun lullube gaskiyar
al’amarin da ƙurar sukuwar dawakansu.
Waƙi’ar kashe Husaini, waƙi’a ce da ta faru tun
shekaru masu yawa da suka wuce. Marubuta
iri-iri, kama daga marubutan tarihi da mawaƙa
da marubutan adabi da al’adu kowa ya yi ta
rubutu a kai, kuma kowa yana zana irin tashi
taswirar yadda waƙi’ar ta kasance. Kusan babu
wani labari mai sanya idanu su rika kwararo da
hawaye da ba a faɓa ba a kai. Duk wani abu
da yake nuna zalunci da rashin imani da
ƙeƙashewar zuciya, da nuna rashin mutunci da
tumasanci, duk sai da aka tattaro su aka zuba
su a cikin labarin wannan waƙi’a. Kai yau da a
ce Miyagun mutanen na da aka yi a tarihi irin
su, Nero ko Genghis khan, ko ma yahudawan
da suka fi su sharri a yau irin su Begin da
Shamir, su ne ake ba da labarin an yi musu irin
abin da masu ba da labarin waƙi’ar Karbala
suke faɗa, to babu shakka sai ka tausaya
musu idan ka ji, sai ka jajanta musu a kai. To
kuma balle a faɗa maka cewa, duk wannan
abu ya faru ne ga ‘ya ‘yan Nana Fatima, jikokin.
Ma’aiki (S.A.W) yaya za ka ji a ranka?!
Wannan shi ne zai sa ka fahimci dalilin da ya
sa muke ganin abin da ake yi a ranar Ashura
game da Husaini irin wanda ba a yi wa Ali ko
Mazon Allah kwatankwacinsa, alhali kuwa sun
fi shi daraja nesa ba kusa ba.
Muna tsakar yawo a garin Hillah ne, sai muka
gan mu a wani babban fili an zageye shi da
katanga, da ƙofar shiga guda ɗaya a buɗe.
Sannan muka ji wani sautin rera waƙe mai cike
da tausayi yana fitowa daga cikin wannan
kango. Muna leƙawa sai kawai mu ga wasu
mutane a ciki zaune babu komai na tufafi a
jikisu in banda abin da suka rufe al’aurarsu
zuwa cibiyoyinsu. Sun bar ƙirajensu tsirara a
waje. A tsakiyarsu sai muka hango wani zaune
sanye da koren rawani (alamar shi Sayyid ne
Ahlul Baiti). Wannan mutum shi ne mai ba da
waƙen, sauran jama’ar dake zagaye da shi
sahu-sahu suna masa amshi.
Daga nan sai abokina Anwar ya tambaye ni
cewa, ko za mu shiga wannan kangon ne? Sai
na ce mu tambayi waɗannan ɗaliban domin su
ne ‘yan gari, su suka fi mu sanin ƙasarsu. Sai
suka ce mana kada mu yarda mu shiga. Ai
kafin mu ankara shi gogan naka Anwar har ya
shige. Daga nan muma muka yanke shawarar
mu bi bayansa.
Mu kwana a nan, za mu ci gaba….