LABARIN SOYAYYAR LAILA
MAJNUN
Waye majnun lailah? Wani mutumne da aka yi a daular banu umaiyya abisazance mafi inganci. Sunansa shine Qais Bn Mulawwah daga kabilar Banu Amir, Qais balaraben kauyene, ya taso tare da ‘yar gidan kawunsa mai suna LAILA
BNT MAHDI IBN SA’D Amfi sanin Laila da sunan Laila Aamiriya, tare suka taso tun suna yara suna kiwon dabobi har suka girma, suka fita daga sahun yara suka kai munzalin balagha.
A Yayin da alamun nuna balaga da cikar budurci suka gama bayyana ajikin Laila sai Qais ya rude soyayyarsa gare ta, hankalinsa ya dugunzuma ya tashi.
Domin a wannan lokacin ne Qais ya
Llura da irin kyawun dirin da Allah ya
yiwa abokiyarsa Laila, a kullum
soyayyar Laila sai kara tashin gwauron zabi take yi a cikin zuciyar Qais, a cikin wannan yanayi ne Qais ya shiga rera
mata waqoqin soyayya kala-kala babu dare babu rana hakance tasa Mahdi mahaifin Laila ya nemi da Qais ya fito dan maganar aure, saboda nuna soyayya da kauna said a Qais ya bayar da raquma hamsin gidansu Laila a matsayin kudin aure.
Ana haka sai ga wani mutum da ake
kira WIRD BN MUHAMMAD wani dan
hamshaqin attajiri ne daga cikin
‘ya’yayen masarautar Banu Umaiyya,
katsahan yayi ido hudu da Laila a wata rana a cikin wani Lambu tana kiwon dabobinta. Daga wannan rana Soyayyar Laila ta hana Wird ya yi bacci a wannan dare! Cikin yan kwanaki kadan Iyayen Wird suka sauka a gidan su Laila dan neman aurenta ga dansu
Wird. A wannan rana da Iyayan Wird
suka je ga mahaifin Laila said a suka
ajiye masa Manyan Raquma guda dari (100) a matsayin kudin aure, wato ribi biyu akan abinda Qais ya bayar! Daga nan lissafi ya kwacewa mahaifin Laila, domin kuwa yayi irin mugun abin kunyar nan na nuna kwadayi da son abin duniya. Bayan haka ne Mahaifin Laila ya kira ‘yarsa Laila cikin daki yanai mata hudunbar cewar ga mai kudi dan masu mulki shi zai aurawa ita! Babbar Magana! Laila taki amincewa da maganar mahaifinta a karon farko, amma sai ya yi mata barazanar cewar zai yanka ta idan har bata amince da auren Wird ba! Kwatsam sai aka wayi gari Qais ya ji gari ya dauka da kace nace din anyiwa masoyiyarsa Laila aure, da Wird. Wanne irin hali Qais zai kasance a wannan ranar? Tun daga wannan lokacin bacci yayi hijira daga idonsa, farin ciki ya gagari zuciyarsa, damuwa bakin ciki gami da bacin Rai da takaici, zubar da hawaye babu dare babu rana,
suka kasance tare da Qais a matsayin abokai na din-din-din!
Wake waken soyayya sune zancensa, bashi da abokin hira sai wakar da yake yiwa laila ga kadan daga irin abinda yake cewa:
zuwa ga Allah nake kai kukan son laila kamar yadda maraya yake kai kukan maraicinsa zuwa a Allah.
Marayanda da kafasa ta karye gashi
kuma dangi sun gujeshe
Lallai rasa iyaye abune mai girman
gaske.
Haka Qais da aka yiwa lakabi da
“Majnunu lailah” yake bin kwararo
kwararo da saman manyan duwatsu da bakin ruwa da cikin furanni yana
rerawa Laila wadannan baituka masu motsa zuciya bai gushe ba harse da akayi masa lakabi da “majnunu laila”....!
Duk da cewa itama Laila tana matukar son Qais(majnun) amma kuma hakan baya hanata ta wahalar dashi, a wasu lokutanma harda yi masa wulaqanci, baya ga yin amfani da mallakeshi da tayi wajen azabtar dashi, dama haka
sha’anin mata yake shi yasa majnun
awani baiti yace:
“Nace da wani babban malami da na
gamu dashi a makka, dan Allah ka bani
labarin wacce take cutar dani,
azamanin da take jiji da kai (saboda ina
sonta) shin hakan da take ba laifi
bane?” Sai Malamin ya fadawa Qais
cewa: “Wallahi da sannu azaba zata
shafe ta kuma a duniya ma saita hadu
da bala’I”. Dagan an Qai yace, sai na
kasa mallakar idona sai da hawaye ya
zubo cikin sauri ya jiqa min aljihun
rigata, sai nace, Allah ya yafe mata
laifinta duk da yake a duniya dan
kadanne samunta.
Qais ko Laila Majnun Bai gusheba a
cikin wannan hali har sai da ya samu
tabin hankali. Domin ya kasance idan
yaga yara suna wasan kasa yakan zauna
tare dasu ya taro kasa ya rinqa gina
gida irin wanda yara suke yi da kasa
yana cewa cikin waqa: “abokaina kuzo
kuga gidana nida laila”....!
A yayinda al-amari ya tsananta sai
mutane suka baiwa mahaifin Majnun
wato Qais shawara da ya daukeshi ya
kaishi ka’aba (dakin Allah) ya umarce
shi da ya roqi Allah ya cire masa son
Laila! Amma saboda tsananin soyayya a
yayin da suka je dakin ka’aba sai
mahaifinsa yace masa: kama tufafin
ka’aba ka roki Allah ya cire maka son
Laila sai Majnun ya kama yace: “Allah
na tuba gareka daga dukkan laifi,
amma bazan tuba daga son da nake
yiwa Laila ba . . . ataqaice haka majnun
ya rayu cikin wannan yanayi na abin
tausayi!
Ita kuwa Laila tuni wanda ya aureta ya
dauke daga kasar Saudiyya gabaki daya
zuwa kasar Iraqi. Haka itama ta rayu
cikin wannan mummunan yanayi
abinka da ‘ya mace mai rauni said a
rashin ganin Qais ya haddasa mata
ciwon zuciya .......! Daga nan ita ma ta
kamu da ciwon zuciya saboda tsananin
soyayyar Qais Majnun! Tana cikin
wannan hali ne na rashin ganin
masoyinta Allah ya karbi rayuwarta! A
lokacin da Majnun yaji labarin
rasuwarta sai da yaje har kasar Iraqi ya
nemi inda take, da inda aka binne ta, a
makabartar da aka binne laila a daidai
gindin kabarinta ya tare.....! Bashi da
aiki sai kuka da wakokin soyayya a
gareta. Wata rana da safe sai masu
wucewa suka hangoshi (Qais-Majnun) ya kifa cikinsa akan qabarinta, ko da aka zo aka duba sai aka tarar Allah ya yi masa cikawa! Haka fa Allah yakejarabtar wasu da soyayya, dan Hakka idan kaji Hasan na sambatu akan Hasana kada ka zargeshi.
Tuesday, 3 January 2017
Majnun Laila
Thursday, 15 December 2016
HALIN DA SHI'A TA JEFA QASAR SYRIA
![]() |
ALLAH KA CECI BAYIN KA NA SYRIA |
Halab Tsohon garine me matuqar girma da muhimmanci ta fuskar tarihi da kasuwanci wanda shine gari na uku mafi girma bayan Istanbul (Qusdandaniyya) da Cairo a zamanin daular Usmaniyya ( othmon empire ).
Hakika duk
Sunday, 11 December 2016
NIGERIAN PEACE CORPS DA AL’UMMAR JIHAR KATSINA
NIGERIAN PEACE CORPS DA AL’UMMAR JIHAR
KATSINA
Kamar yadda mu ka ji kuma mu ka gani cewa
Mahukuntan Nigeria sun gabatar da qudurin su
na sanya wannan hukuma a cikin jerin
hukumomin tsaro na kasar Nigeria. Wannan yazo
a daidai lokacin da matasan kasar ke cikin halin
rashin aikin yi wadda samun damar kan ceci
matasa da yawa a wannan Kasa. Kusan ka iya
cewa jahohi da dama sun yi maraba da wannan
yunkurin na daukar ‘yan peace corps musamman
yadda ‘yan peace corps din suka dade suna ma
kungiyar hidima tsawon shekaru biyar, amman
ban da jiha ta Katsina inda wasu mutane ke ma
‘yan kungiyar kallon mayaudara, kusan kwana
biyar da su ka gabata dan uwa na Husain
Kyar'adua ya yi rubutu don ya bayyana ma
al’ummar jihar Katsina halin da ake ciki a jihar
dangane da kungiyar da kuma kokarin da
Kwamandan su yake na ganin ya ba Katsinawa
hakkinsu. A cikin rubutun nashi wasu masu ganin
cewa su sun waye da kafofin yada labarai na
zamani su kai ta maganganu wadanda za su sa
shakku musamman ga masu sha’awar shiga
kungiyar wanda ga alama basu san komi ba
game da batun.
HALIN DA KUNGIYAR TA KE CIKI A KATSINA
A wajan shekarar 2012 ne kungiyar ta bayyana a
jihar Katsina inda mafi akasarin wadanda su kai
rijista da kungiyar matakin karatun su bai wuce
na Sakandire ba, hakan ne ma yasa mutane
masu zurfin karatu su ka rena aikin suke masu
izgili kala-kala, ban mantawa akwai jajirtattu a
cikin ‘yan Peace corps din wadanda su kai ta
kokarin samar ma kungiyar gindin zama a
wannan jiha wanda karshe wasun su har
makarantun sakandire su kai balantiya suna
zuwa don rage ma malamai aiki, wannan kadan
ne daga jajircewarsu. To abun mamaki wanda
anan gaba zai iya kawo ma tsaffin ‘yan kungiyar
matsala shine rashin samun masu karatu mai
zurfi wadanda za su zama shuwagabanni a
matakin jiha da kasa wanda yanzun maganar da
ake adadin mutane 4000 ne aka ce an ba jihar
amman har yanzun basu samu mutane 500 ‘yan
asalin jihar wadanda su kai rijista ba,ranar
alhamis din da sukai rally akalla wadanda ba 'yan
jihar Katsina ba kusan mutum dari wadanda
galibin su graduate ne su ka zo sukai rijista a
quota Katsina. wannan na gwada cewa karshe
dole a cike gurbin su da ‘yan wasu jihohi
wadanda su ka dau abun da muhimmanci wanda
har an fara hakan.
Kan haka ne Hussain ya so ya jawo hankalin
al’umma cewa ayi himma wajan shiga aikin kada
ace wai sai Shugaban Kasa yasa hannu sannan
za a yi don a lokacin zai iya zama sai mai hanya,
ko kuma mu komo muna cizon yatsa muna zagin
wasu cewa sun kawo mutanen jihar su. Karamin
misali anan NPower ga kuma Civil Defense
wadanda aka rika ce masu kafi banga.
Kira naga al’umma shine mu yi kokari mu shiga
aikin nan don cike gurabun da aka tanadar ma
jihar. Sannan daga karshe ina kira ga duk mai iko
kan tallafa ma matasan jihar, to ga dama ta
samu ta taimakon rayuwar matasa.
An ruwaito cewa a Kano gwamnan su ya biya ma
mutum 2000 kudin shiga haka ma a jihar Yobe ya
biya ma mutum 3000. Mu kuma a jihar mu a na
tai masu yarfe.
ALLAH YA SA AL'UMMAR MU SU FARKA
Hasan Kabir Yaradua ( Hk Yaradua )
11/12/2016
Sunday, 20 November 2016
Gangamin Tallafin Yan Gudun Hijira
#GANGAMINTALLAFINIDPS: GARABASA TA SAMU - HANYAR RAHMA KAI TSAYE!
الراحمون يرحمهم الرحمان ارحموا من فى الأرض يرحمكم من فى السماء
Masu tausayi, Allah Mai Rahma Ya na tausaya ma su. Ku tausayawa bayin Allah a bayan Kasa, sai Allah Mai Rahma da ke Sama Ya yi maku Rahma!
1. SHIN KUN SAN HALIN DA YAN GUDUN HIJIRA KE CIKI A BORNO A YANZU?
Daure ku biyo mu domin ziyarar gani da ido a wurare daban-dabam na 'yan Gudun hijira a Jihar Borno.
2. Ko kun San cewa Al'ummar Musulmin Jihar Kano sun aika Tallafin gaggawa na Trailer 10 ta abinci da Tufafi da qimarsu ta fi #200,000,000 (Naira Miliyan Dari Biyu) kuma mun je mun raba hannu da hannu ga wadanda suka cancanta?
3. Ko Allah Ya sa kuna cikin wadanda suka tallafa da Abinci ko Tufafi ko kudi don wannan aikin?
Ku biyo mu a shafinmu na facebook don ganin hotuna da videos na Al'ummar da muka kai wa tallafin da yanda muka damka amanar da kuka dora mana.
4. Ko ka yi shirin fara bada tallafinka na akalla N1,000 a wata don ceto wadannan bayin Allah daga yunwa da CUTUTTUKA?
Ka na iya turowa kai tsaye ta wadannan lambobin account:
JAIZ BANK 000 0024 550 ko StanbicIBTC 000 123 6900
Sunan Account: Council of Ulama Kano
5. Shin kun shirya bada gudunmawar ku ta wasu hanyoyi daban dabam?
Ku tuntu6e mu kai tsaye:
A. Dr Said Ahmad Dukawa (0701 211 9622) or
B. Engr Basheer Adamu Aliyu (0815 738 3838)
6. Shaitan ya hana ka yin wadancan duka?
Kar ka bari ya hana ka aikawa da wannan sakon ta hanyar facebook ko whatsapp da sauran su.
Manzon Allah Sallallahu Alaihi wa Sallam ya ce "duk wanda ya yi nuni ga alheri zai samu lada kamar wanda ya aikata alherin."
Sunday, 30 October 2016
Abubuwan Da Yariman Saudiya Yayi Kafin Rataye shi
Abubuwan Da Yariman Saudiya Yayi Kafin Rataye Shi-- Darasi Ga Kowa
Ismai'l Karatu Abdullahi
Kasar Saudiya, kasacewarta ta yi ƙaurin suna a duniya kan gudanar da hukuncinta kan gaskiya ga duk wanda ya aikata abunda bai dace ba, tana hukunci ne daidai da abunda ya aikata. Kutunan Saudiya masu adalci ne, basu bambamtawa wajen zartar da hukunci.
Wani abun misali ya faru a ranar 18 ga watan Oktoban shekara ta 2016, inda aka rataye wani basarake ta dalilin kashe wani ɗan Saudiya mazauni ƙasar.
Yariman mai suna Turki Bin Saud Bin Turki Bin Saud Al Kabeer, an rataye shi. An yi masa haka ne daidai da abunda ya aikata kamar yadda dokan ƙasarsu ya kasance.
Yariman, mintuna kaɗan kafin a rataye shi, yayi wasu abubuwa waɗanda za su kasance darasi a gare mu.
Ga kamar yadda ya yi: An Kashe Saud Bin Turki ne bisa kisan gilla da yayi wa wani- Adalci ga Kowa.
Mintuna kaɗan kafin rataye shi, ya nemi a bar shi ya gana da iyalanshi, kuma ya samu. Ya ɗauki kimanin awanni 4 tare da iyayensa da danginsa, ba sai an yi bayanin abunda ya gudana ba kowa zai iya sani kamar yin ban kwana, ƙarfafa masa zunciya da neman gafara.
Daga bisani sai Limamin Masallacin Al Safa ya ce a ɗauko shi daga ganawar da iyalinsa waɗanda suka ta kiran sunanshi suna bankwana , babu abunda za ta ji sai kuka da alamun baƙin ciki.
Muhammad Al Maslookhi ne ya watsa a shafinsa na "Twitter", Su kuma Shafin Saudi "News site Al Marsad", suka ruwaito.
Masu rataya suka ɗauke shi zuwa ofishin 'yan sanda inda nan ne zai rubuta wasiyarsa ta ƙarshe, amma bai iya rubutawa ba.
Da misalin karfe 11 na safe, iyalan wanda Yariman ya kashe, suka iso inda aka sanar da su za a rataye ahi.
Yariman, yayi alwala, sannan ya jira lokacin da za a rataye shi.
Babba wansa, yayi ƙoƙarin magana da iyalin wanda Yariman ya kashe domin nema wa ƙaninsa gafara, da kuma ko zasu karɓi diyya, a yinkuri na karshe kafin a rataye Yariman amma sun ƙi yarda.
Bayan sallar Azahar, 'yan'uwan Yariman suka sake neman wannan alfarman daga iyayen waɗanda aka kashe amma sun ƙi amincewa.
Kamar yadda kuka sani musulunci ba addini ba ne mai danne hakkin kowa ba. Kamar yadda 'yan'uwan Yarima suka nemi iyalan wanda Yarima ya kashe da su karɓi diyya amma suka ƙi, don haka dole a zartar wa Yariman hukunci daidai da abunda ya aikata.
Yarima yayi sallar Azahar da La'asar. Bayan nan da karfe 4:13 aka rataye shi. Har aka rataye shi, babu abinda ya ke fitowa daga bakinshi sai karatun Alkur'ani da ambaton neman yafiya ga Allah.
Kar ku manta, an rataye Yariman ne sakamakon kashe wani da yayi da bindiga.
Addu'armu Allah Ya gafarta wa wanda aka kashe da shi da yayi kashin.
©Zuma Times Hausa
SHUGABA BUHARI YA YI ALLAH WA'AZI DA HARIN YAN SHI'A A DAKIN ALLAH
Shugaba Buhari ya yi Allah-wadai da harin 'yan shi'a a kan Dakin Allah.
Shugaba Muhammadu Buhari ya yi Allah-wadai da harin da aka kai da makami mai linzami kan garin Makkah. Kanfanin Dillacin Labarai na Qasa mai Tsarki, Saudi Press Agency (SPA) ya ruwaito cewa Shugaba Buhari ya kira Sarki Salmanu dan AbdulAziz Alu Sa'ud, inda bayan ya jajanta masa mugun nufin da aka nufi garin na Makkah, ya yi addu'ar Allah Ya ci gaba da tsare garin Makkah da TsarewarSa da dukan Musulmi.
Shi ma Sarki Salman ya roqi Allah Ya taimaki Nigeria Ya kaita ga cin nasara, Ya kuma kareta daga sharrin maqiya.
http://spa.gov.sa/1553765
Haqiqa wannan waya ta Buhari ta qara nuna irin qaunar da Baban ya ke da ita ga Dakin Allah da ma Qasa mai Tsarki.
Allah Ya taimaki Baba Buhari Ya tsare shi da TsarewarSa. Allah Ya tozarta duk masu yunqirin cutar da DakinSa Ya hana musu biyan buqata.
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=1599634673396214&id=100000490902329&ref=bookmarks